Gwamnatin Kano ta Fadi Dalilin Fara Rajistar Gawan da Ake Binnewa a Makabartu

Gwamnatin Kano ta Fadi Dalilin Fara Rajistar Gawan da Ake Binnewa a Makabartu

  • Gwamnatin Kano za ta bude rajista a makabartu domin daukar alkaluman mamatan da ake binnewa da zimmar samun sahihan bayanai kan yawan mutuwa a jihar
  • Kwamishinan lafiya, Dr. Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan a garin Kura inda ake zaton wasu mutum 40 sun rasu kwanakin baya saboda bullar wata cuta
  • Labaran ya ce an dauki matakin ne domin samun tabbacin yawan wadanda ake binnewa, da kuma gujewa labaran karya kan yawan mamatan da ake samu a jihar Kano

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Kano- Gwamnatin Kano ta samar da littafin yin rajistar adadin mamatan da ake binnewa a makabartun dake fadin jihar.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta musanta shirin korar wadanda Ganduje ya dauka aiki

Kwamishinan lafiya a Kano, Dr. Labaran Abubakar Yusuf ne ya tabbatar da daukar matakin yayin taron makon allurar riga-kafi a Afrika a karamar hukumar Kura.

Gwamna Abba Kabir Yusuf
Gwamnatin Kano za ta fara daukar alkaluman wadanda ake binnewa a Kano Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Facebook

Tribune Nigeria ta wallafa cewa kwamishinan ya ce daukar matakin zai taimaka kwarai wajen tantance ainihin adadin wadanda ake binnewa a makabartun.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce wannan daya daga hanyoyin da gwamnati ta bullo da shi ne wajen magance labaran karya kan yawaitar mutuwa a jihar Kano.

Gwamnatin Kano ta magantu kan yawan mutuwa

Kwamishinan lafiya na Kano, Dr. Abubakar Labaran Yusuf ya bayyana cewa sun samu labarin yawan mace-mace a fadin jihar.

Ya ce wasu daga labaran ba gaskiya ba ne, inda ya yi misali da kauyen Gun-dutse da ke kura da aka ruwaito cewa an samu labarin akalla mutane 40 sun rasa rayukansu saboda bullar bakuwar cuta.

Ana yada labaran mace-macen karya a Kano

Leadership News ta tattaro cewa kwamishinan ya musanta hakan, inda ya ce mutum shida ne suka rasu.

Kara karanta wannan

Abba Gida-Gida ya kaddamar da titi mai hawa 3 a kan kudi ₦15bn a Dan Agundi

Dr. Abubakar Labaran Yusuf ya kuma koka kan yadda labaran karya ke kawo cikas wajen gudanar da ayyukan ma'aikatarsa.

A jawabin da ya yi, kwamishinan ya yi kira na musamman ga al'umma su guji yada labaran da ba su da tabbacinsa.

An bayyana dalilin rashe-rashe a Kano

A baya kun ji gwamnatin jihar Kano ta dora alhakin yawaitar rashe-rashe da ake yi a jihar kan tsananin zafin da ake fama da shi.

Kwamishinan lafiya a jihar, Dr. Abubakar Labaran Yusuf ya ce duk da cewa ana tsananta bincike kan musabbabin rasuwar, ba zai rasa nasaba da tsananin zafin da ke tsose ruwan jikin mutane ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng