Jerin Jihohin Najeriya da Arzikin da Kowace Ta Mallaka Ta Fuskar Alkaluman GDP

Jerin Jihohin Najeriya da Arzikin da Kowace Ta Mallaka Ta Fuskar Alkaluman GDP

Abuja - A wata mazhabar, masana ilmin tsimi su kan auna karfin tattalin arziki da ma’aunin GDP wanda shi ne jimillar arziki.

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Alkaluman da aka samu daga shekarar 2022 sun nuna arzikin da kowace jihar kasar nan ta mallaka, inda aka ga Legas ce a gaba.

tattalin arziki
Gwamnonin Jihohin da suka fi kowane karfin tattalin arziki a Najeriya Hoto: Babajide Sanwo-Olu, Sir Siminalayi Fubara, Pastor Umo Eno
Asali: Facebook

Karfin tattalin arzikin jihohin Najeriya

Bayanan da aka samu daga The Cable a dandalin X sun nuna cewa jihohin da suka fi arziki sun yi tarayya a wajen mallakar mai.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Karfin tattalin arzikin Legas kadai ya zarce Naira tiriliyan 40 tun a shekarar 2022. Jihar ce kan gaba wajen samun kudin shiga a yau.

Kara karanta wannan

Kashim Shettima ya fayyace abin da ya tilastawa Tinubu cire tallafin man fetur

Jihohin da ke yankin Neja-Delta; Ribas, Akwa Ibom, Delta da Bayelsa suna sahun gaba.

Legit ta yi nazarin alkaluman, ta lura cewa Ekiti, Ebonyi a Enugu su ne jihohin kudancin kasar nan mafi karancin karfin tattali.

Tattalin arziki: Matsayin jihohin yankin Arewa

A yankin Arewacin Najeriya, jihar Neja ce ake lissafin ta fi kowace karfin arziki, daga nan kuma sai Kaduna da ke makwabtaka da ita.

Benuwai mai arzikin noma ta sha gaban Kano da akalla Naira biliyan 700. Kogi, Katsina da Sokoto ne suka rufe jihohi 20 na farko.

Borno, Nasarawa, Kebbi, Zamfara, Kwara da Yobe sune jihohin da ke karshe idan ana zancen karfin tattalin arziki ta GDP a Najeriya.

Jihohin da suka fi karfin tattalin arziki

1. Lagos: N41.17trn

2. Rivers: N7.96trn

3. Akwa Ibom: N7.77trn

4. Imo: N7.68trn

5. Delta: N6.19trn

6. Anambra: N5.14trn

7. Ondo: N5.10trn

Kara karanta wannan

Yayin da ake ta zarge zarge, Kashim ya kare gwamnatin Buhari, ya fadi tsare tsaren Tinubu

8. Ogun: N5.03trn

9. Bayelsa: N4.63trn

10. Niger: N4.58trn

11. Kaduna: N4.31trn

12. Benue: N4.27trn

13. Kano: N4.20trn

14. Cross River: N4.07trn

15. Edo: N3.99trn

16. Kogi: N3.69trn

17. Oyo: N3.65trn

18. Abia: N3.53trn

19. Katsina: N3.32trn

20. Sokoto: N2.85trn

21. Adamawa: N2.66trn

22. Bauchi: N2.63trn

23. Ekiti: N2.35trn

24. Osun: N2.30trn

25. Ebonyi: N2.24trn

26. Jigawa: N2.16trn

27. Gombe: N2.10trn

28. Taraba: N2.04trn

29. Borno: N1.96trn

30. Nasarawa: N1.86trn

31. Kebbi: N1.80trn

32. Zamfara: N1.73trn

33. Plateau: N1.50trn

34. Enugu: N1.45trn

35. Kwara: N1.38trn

36. Yobe: N1.09trn

<BudgIT 2022>

Tsohon Mataimakin gwamna ya dauke motoci

Rahoto ya zo cewa tsohon mataimakin gwamnan Edo ya tubure, ya ki dawo da motoci bayan 'yan majalisa sun tsige shi a mulki.

Kara karanta wannan

Karin Albashi: Kungiyar TUC ta ba 'yan Najeriya tabbaci kan hauhawan farashin kaya, ta fadi dalilai

‘Dan siyasar ya ce mota guda kurum ya samu a tsawon shekaru kusan takwas mataimakin gwamna a karkashin Godwin Obaseki.

Asali: Legit.ng

Online view pixel