Rudin Soyayya: Rundunar Sojin Najeriya Ta Tabbatar da Jami’inta Ya Kashe Mace Mai Ciki

Rudin Soyayya: Rundunar Sojin Najeriya Ta Tabbatar da Jami’inta Ya Kashe Mace Mai Ciki

  • Rundunar sojin Najeriya ta musanta cewa ta dauki tsohon da Boko Haram aiki bayan an fara yada jita-jita
  • Ta tabbatar da yadda soja daga cikin jami’anta ya kasha wata mata bayan samun sabani a tsakaninsu
  • Rundunar ta tabbatarwa ‘yan Najeriya za ta ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da tsaro da yiwa kowa adalci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Salisu Ibrahim ne babban editan sashen Hausa na Legit. Kwararren marubucin fasaha, harkar kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas

FCT, Abuja - Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kisan wata mata da wani jami’inta ya yi a barikinta da ke jihar Enugu a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya.

A makon da ya gabata ne aka samu rahoton cewa, Muhammad Adamu, wanda aka ce tubabben dan Boko Haram ne da ya shiga aikin soja ya kashe wata mata a barikin Sojan Najeriya na 82 da ke jihar.

Kara karanta wannan

Ke duniya: An kama wani mutum da zargin kashe mahaifiyarsa mai shekaru 100 a Najeriya

Sojoji sun amsa jami'insu ya kashe mata mai ciki a Enugu
Rundunar soji ta amsa jami'inta ya kashe wata mata a Enugu | Hoto: @DefenceInfoNG
Asali: Twitter

Matar mai suna Hauwakulu Tabra, an ce budurwar Adamu ce. An ce tana dauke cikin da wani ya yi mata, wanda hakan ya fusata sojan, Premium Times ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rundunar sojin Najeriya ta yi martani

Da yake martani kan lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, kakakin rundunar, Onyema Nwachukwu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kama Adamu tare da tuhumarsa da aikata kisan kai.

Nwachukwu, ya ce ana zarfin Adamu da kashe matar ne a daren Alhamis kuma an gano gawarta a cikin harabar barikin a ranar Juma’a.

A cewarsa:

“Bincike na farko ya nuna cewa sojan ne ya kashe marigayi Hauwakulu Tabra, wanda a yanzu haka yake tsare don ci gaba da bincike tare da gano dalilin da ya sa ya aikata hakan.”

Adamu ba tsohon dan Boko Haram bane, inji soji

Kara karanta wannan

An sake kai harin da ya yi sanadiyyar kashe mutane 10 a jihar Plateau, jama'a sun shiga firgici

Sai dai, kakakin rundunar ya musanta ikirarin cewa Adamu dan Boko Haram ne da ya tuba, rahoton The Guardian.

Daga nan, ya mika sakon ta’aziyya ga iyalan Hauwakulu tare da bayyana jimamin abin da ya faru.

Kakakin ya kuma tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa za a yi adalci a lamarin domin rundunar ba za ta lamunci duk wani dabi’a ta rashin da’a a cikin jami’anta ba.

Soja ya sha alwashin daukar fansa kan kashe abokan aikinsa

A bangare guda, wani soja mai suna Egitanghan G. ya bayyana cewa za su dauki fansa kan kisan sojoji da aka yi a jihar Delta.

Sojan wanda shi ma ya fito daga jihar Delta ya ce abin takaici ne yadda wasu ke munanan kalamai ga sojojin da suka mutu.

Egitanghan ya nuna damuwa kan yadda abin ya faru duk da sadaukar da rayukansu da suke yi wurin kare kasar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel