Ga Sarauta Ga Kudi: Muhammadu Sanusi II Na Shirin Zama Surukin 'Dan Siyasar Kwara

Ga Sarauta Ga Kudi: Muhammadu Sanusi II Na Shirin Zama Surukin 'Dan Siyasar Kwara

  • Diyar tsohon sarkin Kano Muhammad Sanusi 11, Yusrah za ta shiga daga ciki da hadadden angonta, Abdulmutallib Akintade Shittu
  • Za a daura auren Gimbiya Yusrah da sahibin nata wanda ya kasance Bayarabe a ranar Juma'a, 19 ga watan Afrilu, a garin Kano
  • Akintade Shittu wanda ya fito daga Kwara shi ne Shugaban hukumar tattara bayanan kasa (GIS) na jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura

Gimbiya Khadija Yusrah, diyar tsohon sarkin Kano kuma Khalifan darikar Tijjaniyah a Najeriya, Muhammad Sanusi II za ta shiga daga ciki.

Za a daura auren Yusrah da angonta mai suna Abdulmutallib Akintade Shittu a ranar Juma'a, 19 ga watan Afrilu, a jihar Kano.

Yusrah Sanusi za ta amarce da Shittu
Yusrah Sanusi za ta auri Mutallib Shitu a Kano Hoto: fashionseriesng
Asali: Instagram

Kamar yadda shafin fashionseriesng ya wallafa a Instagram, za a daura auren masoyan ne a mahaifar amarya.

Kara karanta wannan

Kannywood-Nollywood: Mista Ibu da fitattun jarumai 4 da suka mutu a shekarar 2024

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Akintade Shtittu ya kasance Bayarabe kuma Shugaban hukumar tattara bayanan kasa (GIS) na jihar Kwara.

Ga hotunan masoyan a kasa:

Jama'a sun yi martani kan auren 'diyar Sanusi II

cute_fiyyah ta yi martani:

"Ita kuma Bayarabe ta samo ikon Allah Allah Ya sanya alkhairi."

zainabaliyubabayo ta ce:

"Abun burgewa irin wanna abin na burgeni sosai Yarbawa suna da kirki gaskiya."

maamah94 ta ce:

"Ai garama yarabawan ba saki wlh aeta hkr kuma akwai dadi wlh."

saif_made ta yi martani:

"Auren yarbawa fa babu saki kin yi daidai 'yar sarki "

maaiman_catering ta yi martani:

"Allah ya sanya alkhairi ya kade fitina Ameen."

abaya_souk_by_deejah ta ce:

"Kwarai kuwa 'dan uwana daga offa Allah ya albakaci auren."

yasminnamada ta ce:

"Tabarakallahu maa sha Allah."

ohmar_gaddaf:

"Suna ma kama, toh Amin ya Allah "

Kakakin 'yan sandan Gombe ya angwance

Kara karanta wannan

Za a dauke wasu na'urori daga Kwalejin Zaria zuwa Legas? Gaskiya ta fito bayan zargin Dattawan Arewa

A wani labarin kuma, kakakin 'yan sandan jihar Gombe, Mahid Abubakar, ya angwance da kyakkyawar amaryarsa mai suna Nafisa a ranar Asabar, 24 ga watan Fabrairu.

Sai dai kuma, labarin soyayyarsu da jami'in 'dan sandan ya bayar a shafinsa na X a ranar Alhamis, 29 ga watan Fabrairu, shine babban abin da ya dauki hankalin jama'a.

Matashin 'dan sandan ya bayyana cewa ya fara yin arba da Nafisa a 2010, sai dai kuma bai fallasa mata sirrin zuciyarsa ba saboda karancin shekarunta a wancan lokacin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng