Masu Zanga-Zanga Sun Mamaye Majalisar Dokokin Tarayya Saboda Abu 1, bidiyo ya bayyana

Masu Zanga-Zanga Sun Mamaye Majalisar Dokokin Tarayya Saboda Abu 1, bidiyo ya bayyana

  • Masu zanga-zanga sun yi tururuwa a majalisar dokokin tarayya domin nuna bacin ransu kan halin da ake ciki na tsadar rayuwa a Najeriya
  • Shugaban 'yan kwadago ta kasa, Joe Ajaero ne ya yi wa mambobin kungiyarsa jagoranci inda suke kokarin isar da kokensu ga shugabannin majalisar
  • Sun bukaci gwamnatin tarayya da ta yi wani abu a kan mawuyacin hali da tattalin arzikin kasar ya shiga tun bayan cire tallafin man fetur

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura

Babban birnin tarayya, Abuja - Shugaban kungiyar kwadago ta kasa, Joe Ajaero ya jagoranci dubban masu zanga-zanga zuwa majalisar dokokin tarayya, domin nuna bacin ransu kan tsadar rayuwa a kasar.

An gano jami'an hukumomin tsaro daban-daban girke a hanyoyin shiga da fita daga majalisar, musamman ma a bangaren sakatariyar tarayya domin kula da yadda ake tafiyar da zanga-zangar.

Kara karanta wannan

Kungiyar kwadago ta fara gudanar da zanga-zangar gama gari kan tsadar rayuwa

Zanga-zangar 'yan kwadago
Masu Zanga-Zanga Sun Mamaye Majalisar Dokokin Tarayya Saboda Abu 1 Hoto: The Nation
Asali: UGC

Ana sa ran masu zanga-zangar, wadanda ke ta wake-wake za su isar da sakonsu ga shugabannin majalisar dokokin tarayyar, rahoton The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan kwadagon sun yi fatali da gargadi da dama da aka yi masu, sannan suka ci gaba da zanga-zangarsu a kan mawuyacin halin da tattalin arziki ke ciki a kasar.

Wani gargadi DSS ta yi wa 'yan kwadago?

A makon jiya ne hukumar DSS ta yi gargadin cewa wasu mutane na kokarin amfani da damar zanga-zangar da 'yan kwadago suka shirya a ranakun 27 da 28 ga watan Fabrairu, domin tayar da zaune tsaye a fadin kasar.

Daraktan hulda da jama'a na hukumar tsaron farin kayan, Dr Peter Afunanya, ne ya yi wannan kira a cikin wata sanarwa da ya saki.

Ya nemi kungiyar kwadago da ta dakatar da zanga-zangar da take nufin yi kan tsadar rayuwa a kasar don samun zaman lafiya.

Kara karanta wannan

‘Yan kwadago sun yanke matsaya kan hakura da zanga-zanga saboda barazanar DSS

Ya bukaci cewa su nemi hanyar sulhu maimakon yin abin da ka iya haifar da tashin hankali a kasar.

Ga bidiyon zanga-zangar a kasa:

'Yan kwadago sun fara zanga-zangar gama gari

A wani labarin, mun ji cewa kungiyar kwadago ta kasa ta fara gudanar da zanga-zangar gama gari kan mawuyacin halin da tattalin arzikin kasar ke ciki.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa kungiyar TUC ta ce ba za ta shiga wannan zanga-zangar ta 'yan kwadago ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng