Tashin Hankali Yayin da Yan Bindiga Suka Tisa Keyar Babban Basarake

Tashin Hankali Yayin da Yan Bindiga Suka Tisa Keyar Babban Basarake

  • An samu tashin hankali a yankin Orodo da ke karamar hukumar Mbaitoli ta jihar Imo, yayin da yan bindiga suka yi awon gaba da mai martaba Eze Samuel Agunwa Ohiri
  • Yan bindigar sun sace basaraken ne a gaban gidansa a safiyar Asabar, 6 ga watan Janairu
  • An tattaro cewa basaraken, tsohon shugaban sarakunan gargajiya na jihar, na tattaunawa da dan uwansa ne lokacin da yan bindigar suka kawo farmaki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Jihar Imo - Yan bindiga sun yi awon gaba da tsohon shugaban majalisar sarakunan gargajiya na jihar Imo, Mai martaba Eze Samuel Agunwa Ohiri.

An rahoto cewa an yi garkuwa da basaraken ne a gaban gidansa da ke Orodo, karamar hukumar Mbaitoli ta jihar Imo, da misalin karfe 8:30 na safiyar Asabar, 6 ga watan Janairu, rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun shiga har fada sun yi awon gaba da babban basarake

Yan bindiga sun sace basaraken IMo
Tashin Hankali Yayin da Yan Bindiga Suka Yi Awon Gaba da Babban Basarake Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Facebook

A cewar wani ganau, yan bindigar sun kuma yi awon gaba da dan uwan Ohiri, wani dan kasuwa da ke zaune a Amurka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"A safiyar Asabar, Ohiri da dan uwansa daga Amurka, sun yanke shawarar fita a cikin motarsu yayin bikin Kirsimeti domin ziyartan wasu abokansu. Bayan ziyarar tasu, sun dawo.
"Da isarsu gidan Ohiri, sai suka faka motarsu, a wani gefe na harabar gidan, yayin da su biyun suke tattauna batutuwa na karshe kafin su yi bankwana da juna. Wata motar highlander cike da yan bindiga sun sha gabansu sannan suka yi harbi kan mai uwa da wahabi. Sun dura su duka biyun cikin motar sannan suka yi gaba. Sun yi ta hanyar Njaba zuwa Orlu."

Wani ganau ya ce dan uwan Ohiri, Solomon, ya yi nasarar tserewa daga hannun masu garkuwa da mutanen.

Kara karanta wannan

Allahu Akbar: Mutum uku da aka sace sun mutu a kokarin gudowa daga hannun yan bindiga

Yan bindiga sun hallaka mutane a Sakkwato

A wani labarin, mun ji cewa a kalla rayuka tara ne suka salwanta yayin da wasu tsagerun ƴan bindiga suka kai farmaki ƙauyuka huɗu a jihar Sakkwato tun daga ranar Litinin har zuwa ranar Talata.

Ganau sun shaida wa Premium Times cewa maharan sun kuma yi awon gaba da wasu mazauna kauyukan a hare-haren cikin kwanaki biyu kaɗai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng