‘Yan Sanda Sun Damke Wasu Jami’ai 3 Za Su Yi Gwanjon Kayan Gwamnati a Jihar Kano

‘Yan Sanda Sun Damke Wasu Jami’ai 3 Za Su Yi Gwanjon Kayan Gwamnati a Jihar Kano

  • Rundunar yan sanda na jihar Kano ta ka wani Darekta na harkar gudanarwa da ayyuka a ma’ikatar ruwa
  • Abubakar Gambo da wani tsohon abokin aikinsa suna fuskantar bincike a kan daukar kayan gwamnati
  • An rubuta takarda domin yin gwanjon dukiyar jama’a, kwamishinan ruwa ya ce shi dai ba da sunansa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Kano - Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sanar da cewa an cafke wasu ma’aikata da zargin shirin karkatar da kayan al’umma.

Kwamishinan ‘yan sandan Kano, Hussaini Gumel ya shaidawa Daily Trust cewa wadannan jami’ai suna hannu, kuma ana bincike.

Jami'an gwamnatin Kano
‘Yan Sanda sun kama jami'an gwamnatin Kano Hoto: Nasara Radio 98.5 FM
Asali: Facebook

Wadanda aka kama sun hada Darektan gudunarwa da ayyukan yau da kullum na ma’aikatar harkar ruwa, Alhaji Abubakar Gambo.

Kara karanta wannan

Yanzun nan: Gobara ta kama ofishin gwamnan jihar Borno

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sannan akwai Baba Yahaya wanda mataimakin sakataren gudanarwa ne a ma’aikatar harkokin ruwa na gwamnatin jihar Kano.

Na ukunsu shi ne wani tsohon shugaban hukumar tsarin noman rani na KAREFA a karamar hukumar Tudun Wada, Nuhu Mansir.

An samu izinin saida kayan gwamnati a Kano

‘Yan sanda sun cafke su ne bisa zargin rubuta wasikar bogi da ta bada izinin yin gwanjon wasu kaya irinsu tanki da injin rabba ruwa.

Kwamishinan ‘yan sandan ya ce ana tuhumar jami’an gwamnati da yin awon gaba da dukiyar al’umma, wanda hakan ya sabawa doka.

Kano: Kwamishina ya ce babu ruwansa

Tashar Nasara FM ta ce da aka tuntubi Kwamishinan harkar ruwa, Ali Makoda, ya nuna ba ta hannun shi aka fitar da takardar nan ba.

A sakamakon bayanin da aka samu daga Makoda, aka samu kwarin gwiwa cewa ma’aikatan sun karkatar da dukiyar jihar Kano ne.

Kara karanta wannan

Muhimman abubuwa 3 da suka faru gabanin yan Majalisa 27 su sauya sheka daga PDP zuwa APC

Da zarar an gama bincike, kwamisinan ‘yan sandan da ya dage wajen ganin bayan miyagu a Kano ya ce za su gurfanar da su a kotu.

Facakar kudi a gwamnatin tarayya

A gwamnatin tarayya, an ji labari Ministar kasuwanci ta shirya kashe kusan N9bn a 2024, amma ‘Yan Majalisa sun yi mata kaca-kaca.

A shekara mai zuwa, Doris Uzoka-Anite ta yi niyyar zuwa birnin Geneva, za a kashe N1bn a tafiyar, hakan ya sa aka taka mata burki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng