Jerin Lokutan da Sojoji Suka Yi Kuskuren Jefa Bama-Bamai Kan Fararen Hula a Najeriya

Jerin Lokutan da Sojoji Suka Yi Kuskuren Jefa Bama-Bamai Kan Fararen Hula a Najeriya

An sha samun kuskuren kai hare-haren bam a kan fararen hula da ba su san hawa ba su san sauka ba a Najeriya.

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Haren-haren waɗanda ake kuskuren kai wa kan fararen hula dai, ƴan ta'adda da masu tayar da ƙayar baya aka nufa da su.

Sojoji sun jefa bam kan fararen hula
Daga 2017 zuwa sau shida sojoji suna kuskuren jefa bam kan fararen hula Hoto: Stock-trek
Asali: Getty Images

Tun daga shekarar 2017 dakarun sojojin Najeriya, sun yi kuskuren kai hare-haren bam kan fararen hula har sau shida, inda mutane da dama suka rasa rayukansu, rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

Ga jerin lokutan a nan ƙasa:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Harin Rann

A ranar 17 ga watan Janairun 2017, sama da mutum 52 ne suka mutu sannan 120 suka jikkata a wani harin bam da aka kai a sansanin ƴan gudun hijira da ke garin Rann na jihar Borno.

Kara karanta wannan

Kaduna: Rundunar Sojin Ƙasa ta ɗauki laifi, ta faɗi gaskiyar abinda ya jawo jefa bam a taron Maulidi

Harin Damboa a Borno

A ranar 13 ga watan Afrilun 2020, wani jirgin yaƙin sojojin saman Najeriya ya kai harin bam a ƙauyen Sakotoku da ke ƙaramar hukumar Damboa a jihar Borno, inda ya kashe fararen hula 17 da suka haɗa da mata da ƙananan yara.

Harin Kurebe

A cikin watan Afrilun 2022, jirgin sojojin saman Najeriya ya kashe yara shida a ƙauyen Kurebe da ke ƙaramar hukumar Shiroro a jihar Neja.

Bama-baman dai an harbo su ne kan ƴan ta'addan da ke yin sintiri a yankin.

Harin Kunkuna

A ranar 7 ga watan Yulin 2022, wani jirgin yakin sojin saman Najeriya ya kai harin bam a ƙauyen Kunkuna da ke ƙaramar hukumar Safana ta Katsina inda ya kashe mutum 13 da suka haɗa da mata da ƙananan yara.

Harin Doma

A cikin watan Janairun 2023, wasu bama-bamai da jiragen yakin sojin saman Najeriya suka harba, sun kashe mutum 37.

Kara karanta wannan

Jerin haɗurran jiragen Rundunar Sojin Najeriya 4 da suka auku a 2023 tare da dalilai

Harin dai ya auku ne a kan iyakar jihohin Benue da Nasarawa a ƙaramar hukumar Doma ta jihar Nasarawa, inda ya ritsa da mutane ciki har da Makiyaya.

Harin Tudun Biri

A ranar 3 ga watan Disamban 2023, jirgin sojojin Najeriya mara matuƙi ya kashe mutum 85 a ƙauyen Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi a jihar Kaduna, cewar rahoton Trust Radio.

Ahmed Guni Ya Ɗauki Zafi Kan Kisan Tudun Biri

A wani labarin kuma, kun ji cewa sanannan malamin addinin musuluncin nan Sheikh Ahmad Abubakar Gumi, ya yi magana kan harin da sojoji suka yi kuskuren kai wa kan fararen hula a ƙauyen Tudun Biri.

Sheikh Gumi ya yi tir da harin wanda ya halaka fararen hula masu yawa, inda ya bayyana cewa wannan wani lamari ne da ke faruwa a Arewacin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng