A Karshe, Shugaba Tinubu Ya Tsoma Baki, Ya Faɗi Matsayar Najeriya Kan Yakin Isra'ila da Falasɗinu

A Karshe, Shugaba Tinubu Ya Tsoma Baki, Ya Faɗi Matsayar Najeriya Kan Yakin Isra'ila da Falasɗinu

  • Bola Ahmed Tinubu ya yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Isra'ila da Falasɗinu a Gaza
  • Shugaban ƙasar ya buƙaci a koma teburin sulhu, a lalubo hanyar masalaha wajen kawo ƙarshen lamarin cikin gaggawa
  • Ya kuma tabbatarwa masu zuba hannun jari cewa su zuba dukiyarsu a Najeriya cikin kwanciyar hankali domin akwai riba mai yawa

Ahmad Yusuf, kwararren Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Riyadh, Saudi Arabia - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada kiran da Najeriya ta yi na tsagaita wuta cikin gaggawa da kuma lalubo hanyar sansanta rikicin Isra'ila da Falasdinu cikin lumana.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Saudiyya.
A Karshe, Shugaba Tinubu Ya Tsoma Baki, Ya Faɗi Matsayar Najeriya Kan Yakin Isra'ila da Falasɗinu Hoto: NTA News
Asali: Twitter

Tinubu ya yi wannan kira ne ranar Juma'a yayin da yake jawabi a wajen taron Saudiyya da nahiyar Afirka wanda ya gudana birnin Riyadh na kasar Saudiyya, Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

NLC da TUC sun gamu da cikas, kotu ta hana Ƙungiyoyin kwadago tsunduma yajin aiki a Najeriya

Yadda yaƙi ya barke a Gaza

Yaƙi ya barke ne tun bayan lokacin da kungiyar Hamas ta kai farmaki cikin Isra'ila, inda ta kashe mutane 1,400 tare da tsare wasu 2400, a cewar jami'an Isra'ila.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayan haka ne Isra'ila ta lashi takobin murƙushe Hamas, inda ta fara kai harin bama-bamai a Gaza, wanda ma'aikatar lafiya ta ce an kashe mutane 10,500 ciki harda ƙananan yara.

Sai dai ƙasashen duniya na ta kiraye-kirayen a tsagaita wuta, haka nan zanga-zanga ta yawaita don kawo ƙarshen yaƙin ciki harda wadda aka yi a karshen makon nan a Amurka.

Muna maraba da masu zuba hannun jari - Tinubu

Da yake jawabi a wurin taron, shugaba Tinubu ya tabbatar wa masu son zuba hannun jari cewa dukiyarsu na da cikakken tsaro a Najeriya.

Ya ƙara da cewa Najeriya a shirye take tsaf kan kowane irin kasuwanci kana ya basu tabbacin cewa zasu ci riba mai tarin yawa a ƙasar nan, NTA News ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Isra'ila/Hamas: A karshe, Isra'ila ta ji korafe-korafe, ta fitar da sanarwa kan tsagaita wuta

Ɗan Takarar Gwamna Na Jam'iyyar APC Ya Sha da Kyar

A wani rahoton kuma Ɗan takarar Gwamna a inuwar APC a zaben jihar Bayelsa, Mista Sylva, ya sha da kyar a Kotun ɗaukaka ƙara ana gobe zaɓe.

Kwamitin alkatan Kotun, ranar Jumu'a, ya yi watsi da sabuwar ƙarar da aka shigar ana neman hana Sylva takara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262