Wike Ya Kwace Filayen Wasu Tsoffin Gwamnonin PDP a Abuja

Wike Ya Kwace Filayen Wasu Tsoffin Gwamnonin PDP a Abuja

Akalla tsoffin gwamnonin jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) uku ne suka rasa kadarorinsu, yayin da hukumar babban birnin tarayya (FCTA) a karkashin jagorancin Nyesom Wike ta kwace filayensu.

A ranar Alhamis, 21 ga watan Satumba ne hukumar FCTA ta bayar da umurnin kwace filayen a cikin wata sanarwa da aka buga a jaridu, tana mai bayyana cewar an soke su ne saboda sun ki bunkasa filayen ko kuma saba doka a babban birnin tarayya.

Wike ya kwace filayen wasu tsoffin gwamnonin PDP
Wike Ya Kwace Filayen Wasu Tsoffin Gwamnonin PDP a Abuja Hoto: Mr Peter Obi/Nyesom Ezenwo Wike
Asali: Facebook

A lokacin da ya kama aiki a matsayin ministan babban birnin tarayya, Wike ya sha alwashin soke duk wani fili da ya saba dokar amfani da filaye ta Abuja, ba tare da la’akari da wanda abin ya shafa ba.

Daga cikin mutane da kungiyoyi 168 da abun ya shafa harda tsoffin gwamnoni uku da suka yi mulki a karkashin inuwar jam'iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Hawaye Sun Kwaranya Yayin da Ɗalibar Jami'ar Tarayya Ta Mutu a Hanyar Zuwa Kasuwa

Ga jerin sunayen tsoffin gwamnonin a kasa:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

1. Peter Obi

Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu, yana daya daga cikin wadanda umurnin soke filayensu da FCTA ta bayar ya shafa.

Kafin ya koma jam'iyyar Labour Party, Obi ya kasance gwamnan jihar Anambra sau biyu a karkashin PDP. Ya fara a matsayin gwamnan jihar karkashin jam'iyyar All Progressives Grand Alliance a 2006 amma ya kare da PDP a 2014.

2. Liyel Imoke

Ya kasance wani tsohon gwamna wanda ya yi mulki a karkashin PDP kuma yana daga cikin mutanen da Nyesom Wike ya bayar da umurnin soke filayensu.

Imoke ya kasance tsohon gwamnan jihar Cross Rivers tsakanin 2007 da 2016, da shari'o'in kotu a tsakani.

3. Joshua Dariye

Kara karanta wannan

Da Dumi-Ɗumi: Innalillahi, Bene Mai Hawa 20 Ya Rushe Kan Jama'a a Babban Birnin Jihar PDP

Dariye ya yi mulki a matsayin gwamnan jihar Filato karkashin inuwar jam'iyyar PDP tsakanin 2004 da 2007.

An kama shi tare da garkame shi kan wawure kudade. Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya yi masa afuwa.

Wike ya rusa shahararriyar kasuwar kilishi a Abuja

A wani labarin, mun ji cewa ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya sake rusa wata shahararriyar kasuwa a Abuja.

A ranar Litinin, 18 ga watan Satumba ne hukumar babban birnin tarayya (FCTA) ta rusa shahararriyar kasuwar Kilishi da ke yankin Area 1 Abuja, jaridar Punch ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel