Sheikh Faskari Ya Shawarci Mutane Su Kare Kansu Daga Harin 'Yan Bindiga A Katsina

Sheikh Faskari Ya Shawarci Mutane Su Kare Kansu Daga Harin 'Yan Bindiga A Katsina

  • Malamin addinin Musulunci ya shawarci mutane su kare kansu daga hare-haren 'yan bindiga
  • Sheikh Musa Ibrahim Faskari ya bayyana haka ne yayin hudubar sallar Juma'a da aka yada a kafafen sadarwa
  • Malamin ya ce Musulunci ya bai wa mabiya addinin damar daukar makami da kare kansu yayin hare-hare

Jihar Katsina - Fitaccen malamin addinin Muslunci a Katsina, Sheikh Musa Ibrahim Faskari ya shawarci mutane su kare kansu.

Faskari ya ba da shawarar ce ga yankunan da ke fama da hare-haren 'yan bindiga da su dauki makamai don kare kansu.

Faskari ya shawarci mutane su kare kansu daga 'yan bindiga
Sheikh Faskari Ya Shawarci Mutane Kan Hare-haren 'Yan Bindiga A Katsina. Hoto: Sheikh Musa Faskari (Facebook).
Asali: Facebook

Meye malamin ya ce kan hare-haren 'yan bindiga?

Malamin ya bayyana haka ne yayin gabatar da hudubar sallar Juma'a da aka yada a kafafen sadarwa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Tinubu Ya Yi Wa 'Yan Najeriya Babban Alkawari Guda 1, Ya Ce Ko Za A Tsane Shi Sai Ya Gyara Kasar

Ya ce addinin Musulunci ya karfafi mabiya addinin da su dauki makamai don kare kansu idan ana kai musu hare-hare.

Ya ce addinin Musulunci ya bai wa Musulmai damar kare kansu daga addininsu da lafiya da dukiya da iyalai da kuma martabarsu.

Ya bayyana yadda aka mayar da mutane bayi

Ya ce:

"Mu na ganin yadda jami'an tsaro ke cike a yankunan mu amma kuma mu na fama da hare-haren 'yan bindiga.
"'Yan uwanmu sun zama bayin wasu a garuruwansu, su na aikin gona a banza, ba za mu yadda da cin zarafi ba.
"Dukkanmu ba ma son mutuwa kuma ba ma kokarin hada kai don kawo karshen abin."

Jihohin Arewa maso Yamma na fama da hare-haren 'yan bindiga a yankuna da dama, Daily Trust ta tattaro.

A daren jiya da misalin karfe 3 na dare 'yan bindiga sun sace daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke Gusau.

Kara karanta wannan

Da gaske sojoji sun kwace mulki a kasar Kongo? Mun binciko muku gaskiyar batu

'Yan bindigan sun kai farmakin ne a dakunan kwanan dalibai uku inda su ka yi awun gaba da dalibai da dama wadanda ba a san yawansu ba.

'Ya sanda sun cafke wani kasurgumin dan bindiga a Katsina

A wani labarin, jami'an tsaro sun cafke wani dan bindiga mai suna Sa'idu Yaro da aka fi sani da Sabon Jini a jihar Katsina.

Wanda aka kaman ana zargin ya kashe kwamandan 'yan sanda a yankin Dutsen-Ma, ACP Aminu Umar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.