Sanatan NNPP Zai Kashe Fiye da Naira Miliyan 20 Biyawa Dalibai Kudin Jami’a

Sanatan NNPP Zai Kashe Fiye da Naira Miliyan 20 Biyawa Dalibai Kudin Jami’a

  • Rufai Hanga ya zabo dalibai da ke karatu a jami’ar Bayero da ke Kano, ya biya masu kudin karatu
  • Sanatan ya dauki dawainiyarsu ne domin ganin yadda aka kara kudin makarantu jami’o’i a yanzu
  • Tallafin ya shafi ‘yan asalin jihar Kano ta tsakiya da ke aji 2, 3, 4, 5 ko maimaci a jami’ar ta Bayero

Kano - Rufai Hanga ya zabi mutane 200 daga jami’ar Bayero da ke garin Kano, zai taimaka masu da kudin karatu na zangon shekarar nan.

Sanata Rufai Hanga mai wakiltar Kano ta tsakiya a majalisar dattawa ya bayyana haka a shafinsa na Twitter bayan an kara kudin makaranta.

‘Dan majalisar yake cewa samun karatun zamani hakkin mutanen mazabarsa ne ba gata ba.

Sanata
Sanatan Kano, Rufai Hanga da Rabiu Kwankwaso Hoto: @SaifullahiHon
Asali: Twitter
"Na bada tallafi ga dalibai 200 daga jami’ar Bayero da ke Kano a mazabar Kano ta tsakiya!

Kara karanta wannan

Jarumin Gwamna Ya Jagoranci Jami’an Tsaro An Dura Gungun ‘Yan ta’adda Cikin Dare

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Ina cika alkawarin da na dauka na agazawa masu karamin karfi a yayin da ake cikin matsin lambar tattalin arziki a dalilin tashin kudin karatu.
Ilmi hakki ne, ba gata ba."

- Rufai Hanga

Daliban Kano masu rabo sun dace!

Muhammad Sameer Rufai Hanga, ya shaida cewa sai da aka tantance kafin a zakulo wadannan dalibai da ake ganin sun cancanci a tallafa masu.

Da yake bayani a shafin Facebook, Muhammad Rufai Hanga ya ce wadanda su ka nemi tallafin za su iya duba sunansu a cikin jerin da ya fitar.

“Alhamdulillahi yau cikin hukuncin Allah, list din dalibai na Bayero University Kano su 200 wayanda Sen Rufai Hanga ya dauki nauyin biya musu kudin makaranta ya kammala, dan haka duk wayanda akayiwa secreening sa Iya duba sunan su anan, ko kuma portal dinsu da zarar makaranta ta gama aikinta akan list din. Allah ya bada sa’a.

Kara karanta wannan

Orire Agbaje: Bayanin ‘Yar Jami’ar da ta Shiga Muhimmin Kwamitin da Tinubu ya kafa

- Muhammad Rufai Hanga

Daliban da aka zabo sun hada da masu karantar Akanta, Ilmin lafiya, Larabci, Aikin gona, karatun manya, Ilmin shari’a da masu karatun nazarin alkaluma.

Akwai masu karanta ilmin dabbobi, addinin musulunci, Injiniya, tattalin arziki, tarihi, da aikin jarida.

Yadda Sanata ya zakulo mutum 200

Akwai mutane 9 daga Dawakin Kudu, 20 daga Dala, sai dalibai 10 daga mazabun Fagge, akwai kimanin 10 a Garun Malam da kusan 10 daga Gezawa.

A jerin Legit.ng Hausa ta akalla mutum 13 daga Gwale, 15 daga birnin Kano, 21 a yanin Kumbotso, sai 10 Kura da kusan 10 a Madobi da kuma Minjibir.

Baya ga wasu 18 ‘Yan Nasarawa, akwai 17 daga Tarauni sai ragowar 20 daga Warawa da Ungogo.

Abin da mutane su ke fada a kan Hanga

Hakan ya jawowa Sanatan yabo daga masu amfani da shafin Twitter. Irinsu Hameed A. Akande su na ganin Hanga ya bi tafarkin Kwankwasiyya a Kano.

Kara karanta wannan

Ministocin Tinubu: Majalisa Ba Ta Tabbatar da El-Rufa'i Ba, Ta Amince da Mutum 45

Shi kuma wani @Jagabanolu ya na ganin ya kamata a hada da sauran kabilu kamar Ibo, Tibi da Kanuri da ke zama a yankin ko da ba nan ne asalinsu ba.

Munzali Ya'u gumel ya ce: “Allah ya saka maka da alheri”

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng