Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Janye Daga Takara, Ya Bar Wa Wanda Jam’iyya Ta Zaba
- Korarren gwamnan jihar Imo ya ce ya janye daga takarar da ya fito a zaben Nuwamban wannan shekarar ta 2023
- Wannan ya faru ne bayan da jam’iyyar PDP a jihar ta amince da tsayar da dan takarar yarjejeniya gabanin zaben
- Rahoto ya bayyana yadda a 2020 aka tsige gwamnan a kan kujerarsa bayan da aka ayyana shi zababben gwamna
Jihar Imo - Tsohon gwamnan jihar Imo, Emeka Ihedioha ya janye daga jerin ‘yan takarar zaben fidda gwanin gwamna a jam’iyyar PDP a jihar da ke Kudu maso Gabas, Channels Tv ta ruwaito.
A baya, an tantance tare da tace tsohon gwamnan a matsayin daya daga cikin wadanda za su yi takarar zaben fidda gwani gabanin zaben gwamnan jihar na ranar 11 ga watan Nuwamba.
Sai dai, a cikin wata wasikar da ya fitar a ranar 27 ga watan Maris, Ihedioha ya sanar da shugabannin jam’iyyar PDP cewa, ya bayyana amincewarsa da sadaukarwarsa game dan takarar yarjejeniya da PDP ta tsayar.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/2e6b967da4d0123e.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Sakamakon Zaɓen Gwamnoni Na 2023: Jerin Zaɓaɓbun Gwamnoni 5 Da Suka Ci Zaɓe Da Ƙuri'u Mafi Ƙaranci
![Yadda dan takarar PDP ya janye daga takara Yadda dan takarar PDP ya janye daga takara](https://cdn.legit.ng/images/1120/a1280a8fb667f549.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Yadda aka kori zababben gwamnan PDP a 2020
A watan Janairun 2020, kotun koli a Najeriya ta kori Ihedioha daga kujerar gwamnan jihar Imo bayan watanni kasa da bakwai da hawansa mulki, rahoton Premium Times.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A hukuncin da alkalan kotun karkashin jagorancin mai shari’a Tanko Muhammadu sun bayyana Hope Uzodinma na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan na ranar 19 ga watan Maris a 2019 a jihar.
Mai daga kara, Uzodinma ya bayyana cewa, shi ne ya samu kuri’u mafi yawa a zaben amma hukumar zabe ta INEC ta ayyana Ihedioha a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar.
Hukuncin da kotun ta yanke
Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun da ta yanke hukuncin ta ce, an zare kuri’un rumfunan zabe 318 a jihar, inda tace dole a hada dasu cikin sakamakon zaben.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/5353d6029b5903ae.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Innalillahi: Hawaye sun kwaranya, fitaccen dan majalisa a wata jiha ya riga mu gidan gaskiya
Babban kotun ya gamsu da shaidun da wani babban jami’i ya gabatar a gabansa, inda yace kotun kasa ya yi kuskure a hukuncinsa.
Daga baya, Kekere-Ekun ta ayyana Uzodinma a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna tare da kwace takardar shaidar lashe zaben da INEC ta ba dan takarar PDP Ihedioha.
A yau ne aka dakatar da shugaban PDP na kasa, lamarin da ya jawo martani daga tawagar kamfen jam’iyyar.
Asali: Legit.ng