Tinubu Ya Yi Nasara a Rumfar da Ya Kada Kuri’a a Jihar Legas, Atiku Ya Samu Kuri’a 1

Tinubu Ya Yi Nasara a Rumfar da Ya Kada Kuri’a a Jihar Legas, Atiku Ya Samu Kuri’a 1

  • Bola Ahmad Tinubu ya fi kowa yawan kuri'u a mazabar da ya kada kuri'arsa a jihar Legas, inji rahotanni
  • Wanda ya bi masa kuwa, Peter Obi ne, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour ta leburori
  • Atiku ya samu kuri'a daya yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben shugaban kasa a Najeriya

Jihar Legas - Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya lashe zabe a rumfar da ya kada kuri'a a Legas.

An ruwaito cewa, Tinubu ya dirke abokin hamayyarsa a jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar da sauran 'yan takarar jam'iyyu daban-daban.

The Nation ta ruwaito cewa, Tinubu ya yi zabe ne a Ward 3, rumfa ta 85 a Alausa ta Ikeja a jihar ta Legas da misalin karfe 10:20 na safe.

Kara karanta wannan

Sakamakon Zaben Akwatin Datti Baba-Ahmed Ya Fito, Ya Sha Kaye a Hannun Atiku

Yinubu ya ci rumfar zabensa
Dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar APC | Hoto: vanguardngr.com
Asali: Facebook

Adadin kuri'a da masu kada kuri'u

Adadin wadanda aka tantance a rumfar mutum 43 ne, yayin da aka ce akwai mutum 324 da suka yanki katin zabe a rumfar.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Tsohon gwamnan na Legas ya samu kuri'u 33 yayin da PDP ta samu kuri'a 1 tak.

Jam'iyyar Labour ta su Peter Obi kuma ta samu 8 yayin da jam'iyyar matasa ta YPP ta samu kuri'a 1 tak.

A yau ne ilahirin 'yan Najeriya suka fito domin zaban shugaban da zai maye gurbin Buhari da kuma sake zaba ko maye gurbin 'yan majalisun tarayya a fadin kasar.

Zaben bana ya zo da sabon salon da ba haka ake zabe ba a Najeriya, 'yan kasar na ci gaba da bayyana jin dadi da samun natsuwa wajen kada kuri'unsu..

Burina Bola Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa, cewar gwamna El-Rufai

Kara karanta wannan

Da duminsa: Sakamakon Zaben Akwatin Atiku Ya Fito, Ya Lallasa Tinubu da Kwankwaso

A wani labarin kuma, kun ji yadda gwamnan jihar Kaduna ya bayyana fatansa na alheri ga dan takarar APC Tinubu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan ya kada kuri'a, El-Rufai ya ce yana addu'ar Allah ya ba Tinubu nasara a zaben na bana.

Ba wannan ne karon farko da gwamnan ke bayyana goyon bayansa da ga Bola Ahmad Tinubu ba, ya sha fadin hakan a baya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.