Dattijo Ya Tubure, Ya Ce Ba Zai Karbi Tiransfa Ba a Kasuwar da Zai Siyar da Buhun Wakensa

Dattijo Ya Tubure, Ya Ce Ba Zai Karbi Tiransfa Ba a Kasuwar da Zai Siyar da Buhun Wakensa

  • Wani dattijo a kafar sada zumunta ya ba da dariya yayin da yace ba za a dauki buhun wakensa ba a yi masa tiransfa na kudi
  • Dattijon, wanda da alamu a kasuwar hatsi yake ya ce shi dai kudi dumus kawai za a bashi, matukar ana son siyan kasyansa
  • Jama’ar kafar sada zumunta sun yi martani mai daukar hankali bayan ganin bidiyon dattijon da aka yada a kafar Facebook

Wani dattijo dan Arewacin Najeriya ya turje tare da bayyana ba zai karbi kudi ta hanyar tiransfa ba, sai da a bashi a hannu.

Dattijon da ba a bayyana sunansa ba an ganshi a kasuwa yana dariya tare da nesanta bayyana ba zai siyar da buhun wakensa ba sai idan tsabar kudi za a bashi.

A bidiyon da Jaafar Jaafar ya yada a Facebook, an ji lokacin da wani mutum ke tambayar dattijon ko zai amince a tura masa kudi ta banki shi kuwa ya ba da kaya.

Kara karanta wannan

Ikon Allah: Bidiyon Tsohon da Yayi Shekaru 61 ba Bacci Kuma Yana Raye a Duniya

Dattijo ya cije, ya ce sai dai kudi a hannu
Dattijo Ya Tubure, Ya Ce Ba Zai Karbi Tiransfa Ba a Kasuwar da Zai Siyar da Buhun Wakensa | Hoto: Jaafar Jaafar
Asali: Facebook

Cikin dariya da raha, dattijon yace sam ba zai amince ba, shi dai ya ji musu kawai kafin a dauki kayansa.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Mutane da yawa a kafar sada zumunta sun yi raha da ganin wannan bidiyon, wasu sun ce basu ga laifinsa ba, domin a zamanin baya babu irin wannan tura kudi ta baki.

Kalli bidiyon:

Martanin jama’a

Ga kadan daga abin da mutane ke cewa:

Ibrahim Musa Gombe yace:

“Zaizo ya saba ai Bankin ma zuwan shi ba'a yarda dashi ba.”

Musa Muhammad Arewa yace:

“Tsoho yaji sanjin kudin buhari sau biyu kenan. 1984 chanjin kudi. 2022 chanji kudi. Baba Allah ya maka rahma.”

Ibrahim Ayuba yace:

“Jaafar Jaafar a ina ka samo bidiyon kasuwar hatsin Funtua?
“Dattawannan fa mahaifanmu ne aradu.”

Fadila H Aliyu tace:

“Tashin hankali, Baba bai yarda ya bayar da wake a ba shi lambobi ba.”

Kara karanta wannan

Bidiyo: Kare ya Firgita Bayan Yayi Ido 4 da Zaki, Ya Haidye Haushi da ya Fara don Tsoro

Lukman Ibrahim Barau yace:

‘Wallahi ba abun daria bane wannan. Najeriya bamu da wayewar da zamu daina amfani da kudi tsaba.”

Ibrahim G Musa Sheka yace:

“Shiyasa kuwa ai labari ya riskemu kayan abinci na ta sakkowa domin a samu kudi a hannu.”

Jikan Duduwa Funtua yace:

“Allah ya kawo Mana sauki Basu son transfer idan kana da kudi a hannu 13,000 masara”

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.