Hoton Gwamna Sule Yayin da Yake Yi Wa Gawar Dansa Addu’a Kafin a Sada Shi Da Gidansa Na Gaskiya

Hoton Gwamna Sule Yayin da Yake Yi Wa Gawar Dansa Addu’a Kafin a Sada Shi Da Gidansa Na Gaskiya

  • Zukata sun yi nauyi bayan bayyanar hoton Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa yana yi wa gawar dansa na fari addu'a
  • Gwamnan ya rasa babban dansa, Hassan Sule a ranar Juma'a bayan ya yi fama da rashin lafiya a Lafia, babban birnin jihar Nasarawa
  • Wani dan Najeriya mai suna Ayoola wanda ya bayyana cewa jarabtan Allah ya fi dukiya da matsayinmu shine ya saki hoton

Nasarawa - An gano hoton gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, wanda ke jimamin rashi da ya yi a gaban gawar dansa, Hassan Sule yana yi masa addu'a.

An tattaro cewa Hassan Sule ya rasu ne a safiyar ranar Juma'a, 27 ga watan Janairu bayan yar gajeruwar rashin lafiya a garin Lafia, babban birnin jihar Nasarawa.

Gwamna Sule da gawar dansa
Hoton Gwamna Sule Yayin da Yake Yi Wa Gawar Dansa Addu’a Kafin a Sada Shi Da Gidansa Na Gaskiya Hoto: Twitter/@AYOOOLA007
Asali: Twitter

Gwamna Sule yana yi wa gawar dansa addu'a

Kara karanta wannan

Matashi Ya Nemo Tsohon Da Ke Ba Shi Alawa Shekaru 20 Da Suka Wuce, Ya Masa Gagarumin Kyauta

Wani mai alhinin mutuwar, @AYOOOLA007, ya garzaya shafinsa na Twitter don wallafa hoton lokacin da yake yi wa dan nasa addu'a sannan ya roki Allah ya ba iyalin mamacin dangana.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya ce:

"Wannan gwamna ne mai ci yake yi wa gawar babban dansa addu'a. Jarabtan Allah ya fi karfin kudi da matsayin mutum."

Kalli wallafa a kasa:

An tattaro cewa Hassan ya rasu yana da cewaru 36 a duniya.

Jama'a sun yi martani

Wasu yan Najeriya sun garzaya sashin sharhi domin yi wa gwamnan da ahlinsa ta'aziyya.

@naijateddy ya ce:

"Allah ubangiji ya karfafa shi sannan ya ba iyalin dangana. Babu uban da ya cancanci binne dansa. Kamata ya yi abun ya zama akasin haka."

@hafidaibrah ta ce:

"Allah ya gafarta masa ya kuma ji kan mamacin, Allah SWT ya ba masoyansa hakuri sannan ya basu juriyar wannan rashi, aameen."

Kara karanta wannan

Gwamna Sule: Jajiberin 'Dana Zai Rasu, Na Dinga Rarrashin Mahaifin da ya Rasa Yara 9 da Shanu 70 a Tashin Bam din Nasarawa

Paul Ikenna Esq. ya ce:

"Wannan hoton na daya daga cikin mafi tsuma zuciya da na taba gani."

Toyin. SM. Adeyemi ta yi wa iyalin addu'a:

"Ya Ubangiji ka ji kansa...ka ba mahaifinan da ahlinsa hakuri. Iyaye basu cancanci fuskantar irin haka ba. Ina mai mika ta'aziyyata. Ina mai baka hakurin wannan rashi."

A wani labari na daban, gwamnatin jihar Edo zata fara rufe masallatai da cocina da sauran wurare idan har basu dauki matakin hana fitar sauti daga gine-ginensu ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel