Peter Obi Zai Kai Ziyara Arewa, Zai Gana da Shugabannin Addinai da Sarakuna a Jihar Kaduna

Peter Obi Zai Kai Ziyara Arewa, Zai Gana da Shugabannin Addinai da Sarakuna a Jihar Kaduna

  • Jihar Kaduna za ta yi babban bako, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour zai kus-kus da malaman addini
  • Hakazalika, rahoto ya ce Peter Obi zai zauna da Sarkin Zazzau da na Jema'a duk dai a jihar ta Kaduna da ke Arewa maso Yamma
  • Peter Obi na ci gaba da fadada takararsa da neman goyon bayan manyan mutane a yankin Arewacin Najeriya da Kudancinta

Jihar Kaduna - Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour, Peter Obi zai yi zaman tattaunawa da shugabannin addinai a yankin Kaduna ta Kudu, kana zai ziyarci sarakuna a yankin.

Hakazalika, Obi zai gudanar da wani taron gangami a filin wasa na Ahmadu Bello da ke Kaduna, inda zai gana da dalibai daga makatrantu daban-daban da kuma ‘yan a mutun jam’iyyar da magoya bayansa.

Kara karanta wannan

Atiku Ya Tona Asirin Manyan Yan Takara Biyu, Yace Hatsari Ne Babba a Zabe Su a 2023

Wannan na fitowa ne daga bakin kakakin jam’iyyar, Dr Yunusa Tanko a yayin wata gwarya-gwaryar zama a jihar Kaduna, Daily Trust ta ruwaito.

Peter Obi zai zauna da sarakuna biyu a Arewa
Peter Obi Zai Kai Ziyara Arewa, Zai Gana da Shugabannin Addinai da Sarakuna a Jihar Kaduna | Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

Obi zai gana da Sarkin Zazzau da na Jema'a

Ya kuma bayyana cewa, Obi zai kai ziyara zuwa fadar Sarkin Zazzau, Amb, Ahmad Nuhu Bamalli da kuma Sarkin Jema’a a Kafancan da ke yankin Kudancin jihar.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Dr Tanko ya kuma bayyana cewa, a yayin taron na kamfen, Obi zai karanto manufofinsa bakwai da yake son cimmawa idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben bana.

Peter Obi na ci gaba da tallata kansa da manufofinsa ga ‘yan Najeriya, hakazalika, yakan fadi maganganu da nuna nagarta da kwarewarsa a mulki.

Obi ya sha bayyanawa ‘yan Najeriya cewa, shi ya cancanci ya gaji Buhari a zaben bana, lamarin da ke kara daukar hankali a kasar.

Kara karanta wannan

2023: Bidiyon Yadda Aka Ceci Fitaccen Dan Takarar Shugaban Kasa Daga Tulin Jama'a Ya Fito

A tun farko, ya dauko abokin takararsa daga Arewacin Najeriya kuma dan jihar Kaduna, Dr Datti Baba-Ahmed.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.