Jihohi 10 Mafi Zaman Lafiya a Najeriya: Cikakken Jerinsu
- Matsalar rashin tsaro a Najeriya ta zama ruwan dare inda kusan ko wani yanki na zama da ita tsawon kimanin shekaru goma yanzu
- Sabon rahoton binciken da aka saki ranar Lahadi, 8 ga Junairu ya lissafa jihohi goma mafi zaman lafiya
- Jihar Ekiti dake yankin kudu maso yammacin kasar ne ya zo na daya cikin jeringiyar
Yayinda Najeriya ta shiga watan farko na sabuwar shekara kuma saura wata guda zaben 2023, Najeriya na cike da tsoro da fargaba bisa matsalar tsaro da ta addabi kasar.
Matsalar tsaro ta zama kayar wuya ga dukkan sassan Najeriya kuma ana fargabar gada abin yayin tsamari lokacin zabe.
Yayinda yankin Arewa maso yamma, Arewa maso tsakiya, da kudu maso yamma, ke fama da matsalar da yan bindiga masu garkuwa da mutane, yankin kudu maso yamma na fama da ta'addancin IPOB, sannan Arewa maso gabas matsalar Boko Haram/ISWAP.

Kara karanta wannan
Kwararan Dalilai 5 Dake Nuna Cewa Wajibi CBN Ya Dage Ranar Daina Amfani da Tsaffin Takardun Naira
Sabon binciken da Statisense ya saki ranar Lahadi, 8 ga Junairu ya bayyana adadin wadanda aka kashe a jihohin Najeriya a 2022.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Asali: UGC
A cewar rahoton da Statisense ya fitar, jihohi 10 ne kacal cikin jihohin Najeriya 36 suke da zaman lafiya.
Cikin wadannan jihohi akwai na Arewa biyar, na kudu 5.
Jihar Ekiti ce ta ciri tuta matsayin jihar da aka samu kisan mutu 6 kacal sanadiyar rashin tsaro a tsawon shekarar 2022.
Jihar Kano, Gombe, Adamawa da Kano da Jigawa ne jihohin Arewa da suka samu shiga jerin.
Ga jerin jihohin nan:
S/N | Jihohi | Adadin wadanda aka kashe |
1 | Ekiti | 6 |
2 | Gombe | 12 |
3 | Adamawa | 17 |
4 | Kano | 17 |
5 | Jigawa | 20 |
6 | Nasarawa | 20 |
7 | Akwa Ibom | 29 |
8 | Bayelsa | 31 |
9 | Oyo | 41 |
10 | Osun | 46 |

Kara karanta wannan
A Gaban Buhari a Yobe, Bola Tinubu Ya Faɗi Matakin da Zai Dauka Kan ASUU Idan Ya Ci Zaben 2023
Asali: Legit.ng