Gwamnatin Ganduje Za Ta Karasa Titi Zuwa Kauyen Kwankwaso da Wasu Ayyuka a Kano

Gwamnatin Ganduje Za Ta Karasa Titi Zuwa Kauyen Kwankwaso da Wasu Ayyuka a Kano

  • Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya amince a kara kudin aikin titin Kwanar Kwankwaso zuwa Kwankwaso
  • Titin da ake gyarawa a karamar hukumar Madobi zai taimakawa mutanen Rabiu Kwankwaso wanda ya yi Gwamna
  • Kwamishinan yada labarai yace an amince da kwangilolin wasu ayyuka da za ayi a kananan hukumomin da ke Kano

Kano Majalisar zartarwa ta jihar Kano ta amince da canjin kudi da aka samu wajen kwangilar hanyar Kwanar Kwankwaso-Kwankwaso a Madobi.

Jaridar Leadership tace kwangilar titin nan da aka bada a farkon shekarar nan a kan N372.268 ya kara kudi, gwamnatin Kano za tayi cikon N97.826m.

Tuni an biya N154.491m, kuma har aikin ya kai rabi domin 'yan kwangila sun yi 50% a garin da tsohon Gwamnan jihar, Dr. Rabiu Kwankwaso ya fito.

Kara karanta wannan

Kwankwaso Ya Kai Takararsa Zuwa Ketare, Zai Gana da Muhimman Gwamnatin Amurka

Da ya zanta da manema labarai bayan taron majalisar zartarwa da aka yi a garin Kano, Kwamishinan yada labarai yace an sake duba kwangilar.

Kudin aiki ya tashi saboda tsadar kaya

An rahoto Malam Muhammad Garba yana cewa yawan tashin farashin kayan gine-gine ya jawo kudin da za a kashe wajen aikin ya karu, ya kai N470m.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Muhammad Garba ya sanar da manema labarai cewa Gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta amince a fitar da N40.373m domin samar da hasken wuta.

Gwamnan Kano
Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje Hoto: @aaibrhim1
Asali: Facebook

Za ayi amfani da kudin ne domin gyara ban-dakoki da ke kasuwanni kauyuka a jihar Kano. Akwai ban dakin kasuwanni 72 da suke amfani da hasken rana.

Aikin da ake yi a yankin Hotoro

Kwamishinan ya nuna za a amince da canjin kudin aikin da aka samu na katafaren titin Muhammadu Buhari da ake ginawa a kan titin zuwa Maiduguri.

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: Sojoji sun kama wasu kudade N19.5 a hannun abokan 'yan bindiga 5 a Arewa

Garba yace aikin ya kai 97%, har an bude gadojin sama da kasa ga wadanda ke bi ta hanyar. Za a kashewa aikin N9.231bn saboda CCTV, katanga da ciyawa.

A rahoton Channels TV, an fahimci za a fadada kwalejin koyon aikin tsabta domin a rika koyar da sababbin ilmomin da hukumar NBTE ta bada dama a kawo.

Za ayi amfani da filin SUBEB da ke Sabuwar Kofa a matsayin bangaren makarantar. Baya ga haka an amince a biya wasu alawus ga malaman jami’ar YMS.

Zanga-zanga a New Nigeria Peoples Party

Rahoto ya nuna 'Dan takaran Majalisa ya bayyana Sulaiman Othman Hunkunyi a matsayin wanda zai kashewa ‘Yan jam’iyyar NNPP kasuwa a zabe.

Wasu sun ce idan da hali, NNNP ta canza ‘dan takaran Gwamnan jihar Kaduna, idan ba haka ba zai yi wahala jam’iyya mai kayan dadi ta kai labari a badi.

Kara karanta wannan

Jami'iyar APC Nakasu Kawai Ta Kawo A Nigeria Tsawon Lokacin da ta Shafe Tana Mulki, Atiku

Asali: Legit.ng

Online view pixel