Wani Ministan Ya Ci Alfarmar Buhari, Ya Samu Sarauta Mai Daraja a Masarautar Daura

Wani Ministan Ya Ci Alfarmar Buhari, Ya Samu Sarauta Mai Daraja a Masarautar Daura

Sarkin Daura, Faruk Umar Faruk, ya zabi karamin Ministan man fetur, Timipre Sylva, zai ba shi sarauta

Timipre Sylva zai zama Sarkin Kudun Hausa saboda rawan da ya taka a gwamnatin Muhammadu Buhari

Tsohon Gwamnan ya yi wa Mai martaba Faruk Umar Faruk alkawarin cewa zai sauke wannan nauyi

Katsina - Mai martaba Sarkin Daura, Dr. Faruk Umar Faruk ya zabi karamin Ministan man fetur, Timipre Sylva, domin ya ba shi sarauta a kasarsa.

Rahoton da Vanguard ta fitar ya bayyana cewa Sarkin Daura ya sanar da Timipre Sylva wannan a wata wasika da ya rubuta, ya kuma damka masa.

Sarkin ya shaidawa Ministan cewa zai ba shi sarautar “Sarkin Kudun Hausa”, a lokacin da ya kai ziyara ta musamman zuwa fadarsa da ke Daura.

Kara karanta wannan

Alkawarin Aure: An Fara Gabatar da Shaidu Kan Hadiza Gabon a Kotun Shari'ar Musulunci

Dr. Faruk Umar Faruk yake cewa tsohon gwamnan na Bayelsa ya samu wannan sarauta saboda cigaban da ya kawo, musamman a yankin Arewa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

This Day tace Basaraken ya fadawa Sylva daga yanzu yana wakiltar mutanen Arewacin Najeriya a yankinsa na Kudu maso kudancin kasar nan.

“Ina farin cikin sanar da kai cewa an ba ka sarautar ‘Sarkin Kudun Hausa’ domin godewa gudumuwar da ka ke ba ‘danmu, shugaban kasa Muhammadu Buhari, GCFR, Bayajida II.
Ministan fetur
Ministan fetur, Timipre Sylva Hoto: tribuneonlineng.com
Asali: Twitter

Nasarorin da ka samu a ma’aikatar man fetur, abin-a-yaba ne, baya ga irin cigaban da kawowa Najeriya, musamman Daura. Za a sanar da kai ranar da za ayi maka nadin sarautar.”

- Sarkin Daura

Sarautar Hausa sai wane da wane

Rahoton yace Sarkin ya shaidawa Ministan cewa duk kasar Hausa, masarautarsa ce kadai take iya bada sarautar Hausa ga wanda aka ga ya dace.

Kara karanta wannan

Inyamuri ba zai gaji Buhari ba, gwamnan yankin Kudu ya bayyana dalilai

A gefe huda, Sylva ya ji dadin wannan karramawa da masarautar mai tsohon tarihi tayi masa. Katsina Post ta fitar da wannan labari a rahotonta.

Ministan na man fetur ya nuna cewa daga yanzu zai dage wajen ganin ya sauke nauyin da aka damka masa na zama Sarkin Kudun kasar Hausa.

Bello Turji

Kun samu labari cewa kasurgumin ‘Dan bindiga, Bello Turji da wasu yaransa sun je yin sallah ne a sa’ilin da sojoji suka yi luguden wuta a sansaninsu.

Da alama Sojoji za su cigaba da addabar yankin da ‘yan bindigan suke. Hantar mutanen da ke wadannan kauyuka ta kada yayin da Turji ya shal.

Asali: Legit.ng

Online view pixel