Ba zan sa a sake Kanu ba: Buhari ya yi watsi da bukatar shugabannin Igbo

Ba zan sa a sake Kanu ba: Buhari ya yi watsi da bukatar shugabannin Igbo

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi watsi da bukatar shugabannin Igbo kan batun sakin Nnamdi Kanu
  • A yau ne shugaban ya gana da shugabannin yankin Kudu, inda suka bijiro da batutuwa da suka shafi yankin ciki har da na Kanu
  • Shugaba Buhari ya ce kamata ya yi a bar kotu ta bayyana adalcinta kan Nnamdi Kanu domin ganin yadda za ta kaya

Ebonyi - Shugaban kasa Muhammadu Buhari, a ranar Juma’a ya yi kira ga shugabannin Kudu-maso-Gabas da su kyale shari’ar da ake yi a kotu ta shugaban IPOB, Mazi Nnamdi Kanu a kasar.

Buhari ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi da shugabannin yankin Kudu maso Gabas da suka hada da shugabannin kungiyar Ohanaeze Ndigbo a sabon gidan gwamnati da ke Abakaliki, Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan

'Batanci: Bayan Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Deborah a Sokoto, Osinbajo Ya Yi Magana Da Kakkausar Murya

Martanin Buhari ga shugabannin Igbo kan rokonsu na a saki Nnamdi Kanu
Ba zan sa a sake Kanu ba: Buhari ya yi watsi da bukatar shugabannin Igbo | Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Shugaban wanda ya kammala ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jihar a yau Juma'a, ya yi nuni da cewa matakin da kotu ta dauka kan lamarin Kanu shi za a bi.

Buhari ya kuma nuna rashin jin dadinsa kan yadda ake ta fama da matsalar rashin tsaro a kasar, inda ya ce duk wanda da aka gani dauke da bindigar AK 47 a kowane yanki na kasar nan, to a yi masa kallon dan ta'adda matukar ba jami'in tsaro bane.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A bangare gudam ya kuma yabawa Gwamna David Umahi bisa ayyukan canza rayuwa da gwamnatin sa (Umahi) ta aiwatar, kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito.

Ka saki Nnamdi Kanu: Shugabannin Igbo sun kalli Buhari ido da ido, sun roki alfarma

A wani labarin, shugabannin yankin Kudu maso Gabas sun bukaci da a gaggauta sakin shugaban tsagerun IPOB, Nnamdi Kanu daga tsare shi da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi.

Kara karanta wannan

2023: Igbo Ba Abin Yarda Bane, Ba Mu Amince Su Mulki Ƙasa Ba, Ƙungiyoyin Arewa

Shugabannin sun yi wannan roko ne a wata tattaunawa da suka yi da Buhari a zauren majalisar zartarwa da ke gidan gwamnati a Abakaliki, babban birnin jihar Ebonyi, inji rahoton Punch.

Buhari ya kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jihar Ebonyi, kamar yadda rahotanni daga fadar shugaban kasa da gwamnatin Ebonyi ta bayyana, The Nation ta ruwaito.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.