Zo Ka Nemi Aiki: Dan Najeriya Ya Nemo Kamfanin da Ke Biyan Albashin Naira Miliyan 3 Duk Wata
- Dan Najeriya ya fadi wasu ayyuka guda biyu da mutum zai iya nema wanda ke biyan naira miliyan uku duk wata
- Kamfanonin dai na aiki ne a Abuja kuma suna neman kwararre da zai kama aiki a guraben da zai samu kudade masu yawa
- Mutane da yawa sun karyata bayaninsa, sai dai jim kadan bayan da ya tura adireshin kamfanonin, an tabbatar da ikirarinsa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Wani dan Najeriya ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa akwai guraben aiki da za a biya albashin naira miliyan uku duk wata.
Mutumin mai amfani da sunan @3mbeeeee a Twitter ya bayyana cewa a Abuja ake yin aikin kuma kamfanonij na neman kwararru da za su kama aiki nan take.

Asali: Getty Images
Sai dai da yawa ba su gamsu da wannan bayanin na sa ba, inda daga bisani ya wallafa adireshin neman aikin don tabbatarwa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jaridar Legit ta tattaro cewa kamfanin na neman kwararru a fannin 'warware rikici' da kuma 'mawallafi kan kyawun halittu'
Ana iya samun karin bayanai kan ayyukan anan da nan.
Duba wallafarsa a kasa:
Ma'aikatan tarayya 2,000 sun rasa albashin watan Nuwamba
A wani labarin, kun karanta cewa akalla ma'aikatan gwamnatin tarayya dubu biyu ne suka rasa albashin su na watan Nuwamba, kamar yadda majiya mai tushe ta bayyana hakan a ranar Litinin.
Wani ma'aikaci gwamnati a ma'aikatar tsaro ta kasa, ya yi nuni da cewa da yawa daga cikin ma'aikatan da ke aiki a ma'aikatar ba su samu albashin su ba, Legit Hausa ta ruwaito.

Kara karanta wannan
Kotu ta garkame lebura wata 7 a gidan gyaran hali kan satar agwagi guda 3 a Filato
Ma'aikacin gwamnatin ya kuma yi nuni da cewa gaza samun albashin ba zai rasa nasaba da tantancewa da ofishin shugaban ma'aikatan tarayya da ke yi a kasar ba.
Da gaske gwamnati ta yi gwanjon babban otel mallakin jihar Kwara?
A wani labarin na daban, a yayin da ake ci gaba da yada jita-jitar cewa an cefanar da babban otel mallakin jihar Kwara, gwamnatin jihar ta fito ta yi martani akai.
Gwamnatin jihar ta ce babu wani dalili da zai saka a sayar da otel din, kawai ta yi gwanjon kayan cikinsa ne don yin gyare-gyare.
Asali: Legit.ng