Tijjani Gandu Ya Fadi Gaskiyar Alakar da Ke tsakaninsa da Jaruma Maryam Booth

Tijjani Gandu Ya Fadi Gaskiyar Alakar da Ke tsakaninsa da Jaruma Maryam Booth

  • Bayan ce-ce-ku-cen da aka samu a kafofin sadarwa na zamani, Tijjani Gandu ya fito fili, ya fadi alakar da ke tsakaninsa da jaruma Maryam Booth
  • Fitaccen mawakin ya ce shi da Maryam sun dauki wasu hotuna da suka jawo rudani a yanar gizo har lamarin ya so ya wuce gona da iri
  • A wata tattaunawa da aka yi da shi, Tijjani Gandu ya ce dama can ya san Maryam, tare da fadin gaskiyar abin da ya sa suka yi hotunan

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Shahararren mawaƙin siyasa, Tijjani Gandu ya fito fili, ya fadawa duniya gaskiyar alaƙar da ke tsakaninsa da jarumar Kannywood, Maryam Booth.

Wannan na zuwa ne bayan da wasu hotunan Tijjani Gandu tare da Maryam Booth masu kama da na aure suka yaɗu kamar wutar daji a soshiyal midiya.

Kara karanta wannan

Wani bam ya tarwatse da mutane a Banki, an samu asarar rayuka a jihar Borno

An ji ta bakin Tijjani Gandu game da alakar da ke tsakaninsa da Maryam Booth.
Hotunan Tijjani Gandu da jaruma Maryam Booth da suka jawo ce-ce-ku-ce a soshiyal midiya. Hoto: Arewabeauty
Source: Facebook

Tijjani ya yi martani kan hotuna da Maryam Booth

Tijjanin Gandu, wanda kuma shi ne mai ba gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf shawara kan al'adu, ya shaida wa TRT Afrika Hausa gaskiya game da alakarsa da Maryam Booth.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A hirar da suka yi ta wayar tarho, Tijjani ya bayyana cewa:

"Zan yi bayanin abubuwan da suka faru satin da ya gabata, kasancewar ganin hotuna na da Maryam Booth, abokiyar aiki. Wadannan hotunan sun jawo ce-ce-ku-ce.
"Har yanzu wasu ba su gane gaskiyar wannan lamari ba. Na ga ya dace, kamar yadda kuka tambaya, in yi maku bayani.

Mawaki Tijjani Gandu ya bayyana cewa shi wannan lamari, watau hotunan da aka ga ya dauka da Maryam Booth, aiki ne suka yi na waka da jarumar.

Dalilin ganin hotunan Maryam Booth da Tijjani Gandu

Fitaccen mawakin, ya bayyana dalilin da ya sa ya dauki hotunan da suka yi kama da na kafin aure da jaruma Maryam Booth, yana mai cewa:

Kara karanta wannan

Albishir da ministan tsaro ya fara yi ga 'yan Najeriya bayan shiga ofis a Abuja

"Shi wannan aiki ne muka yi, aiki irin na waka, kasancewata mawaki, bangare-bangare, to wannan waka ce aka yi ta 'Amarya Mai Capacity,' muke so mu fito da bidiyonta ta wani irin salo, shi ya sa muka shirya wannan.
"Kuma an dauki wadannan hotuna ne da ku ke gani suna yawo a lokacin da aka dauki wannan waka, kuma hotunan aka fara saki. An yi abin ne saboda raha, a dan ja hankali, to sai kuma abin yake nema ya wuce gona da iri."

Mawakin ya jaddada cewa an dauki hotunan ne kawai saboda aiki, kamar yadda aka saba ganin jaruma da jarumi suna yi don tallata wani bidiyo ko fim da za su saki.

Mawaki Tijjani Gandu ya ce akwai alaka mai kyau tsakaninsa da Maryam Booth amma ba ta soyayya ba.
Hotunan Tijjani Gandu da jaruma Maryam Booth da suka jawo ce-ce-ku-ce a soshiyal midiya. Hoto: Arewabeauty
Source: Facebook

Alakar Tijjani Gandu da Maryam Booth

Game da jita-jitar da wasu ke yadawa, cewa Tijjani Gandu zai auri Maryam Booth ne, shi ya sa suka yi wadannan hotunan, mawakin ya ce ko kusa ba haka ba ne.

"Masu tambayar me ya sa ba a dauko wasu jarumai ba, aka dauko ita Maryam Booth, to kasancewar idan za ka yi aiki, kana duba yiwuwar wa ya fi cancanta ka dauko, ko kuma waye zai ba ka abin da kake nema, shi ya sa muka dauko wannan jaruma.

Kara karanta wannan

Kuɗin da yawa: Gwamna Zulum ya faɗi biliyoyin Naira da ya kashe kan tsaro a 2025

"Baya ga haka, kamar yadda ku ke gani, ita jarumar ta ba da yanayin abin da ake bukata. Masu tambaya cewa kuma muna da wata alaka ne ta soyayya, ko kuma dama can mun san juna, to maganar gaskiya dama can mun san juna amma babu wata alaka ta soyayya da ke tsakaninmu."

- Mawaki Tijjani Gandu.

Kalli bidiyon tattaunawar a nan kasa:

'Na gaji da tambayoyi kan aure' - Maryam Booth

A wani labari, mun ruwaito cewa, jaruma Maryam Adamu wacce aka fi sani da Maryam Booth ta magantu a kan yawan tambayar da ake yi mata na 'yaushe za ki yi aure?."

Maryam Booth ta ce shi aure nufi ne na Ubangiji, kuma duk yadda mutum ya kai ga shirin aure idan Allah bai yi lokacin nan ba toh babu yadda za kayi.

Hakazalika, jarumar ta koka kan yadda mutane ke yawan tambayar ta dalilin da ya sa ta rame, tana mai cewa, mutuwar mahaifiyarta ta gigita ta sosai, don haka dole ta rame.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com