Iran Ta Yi Wa Isra'ila Ɓarna bayan Harin Makami Mai Linzami da Ta Harba Ƙasar

Iran Ta Yi Wa Isra'ila Ɓarna bayan Harin Makami Mai Linzami da Ta Harba Ƙasar

  • Wani asibiti a Beersheba, Isra’ila ya gamu da hari yayin da Iran ta harba makamai masu linzami, lamarin da ya jikkata mutane da dama
  • Ministan tsaron Isra’ila ya ce “ba za a bar Ayatullah Ali Khamenei ya ci gaba da rayuwa ba,” saboda hare-hare
  • Sojojin Isra’ila sun kai farmaki kan sansanonin nukiliyar Iran da suka hada da Arak da Natanz, yayin da Iran ke fargabar hare-haren Amurka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tel Aviv, Israel - Harin da kasar Iran ta kai wa Isra'ila ya jawo mata asara yayin da ake ci gaba da rikici.

Wani asibiti a garin Beersheba na Isra’ila ya gamu da hari yayin da kasar Iran ta harba makamai masu linzami.

Iran ta kai hari Isra'ila inda ta jikkata mutane
Harin Iran ya ruguza wani asibiti a kasar Isra'ila. Hoto: Getty Images.
Source: Getty Images

An samu raunuka da Iran ta farmaki Isra'ila

Rahoton BBC News ya ce Iran ta ce harin ya nufi wani sansanin soja kusa da asibitin, ba asibitin kansa ba.

Kara karanta wannan

Donald Trump ya yi magana kan yiwuwar shiga faɗan Iran da Isra'ila da ake yi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyi sun tabbatar da cewa an samu raunuka a sassa daban-daban na Isra’ila sakamakon harin da aka kai.

Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce:

“Ba za a bar Khamenei ya ci gaba da rayuwa ba.”

A lokaci guda, rundunar sojojin Isra’ila ta ce ta kai farmaki kan sansanonin nukiliyar Iran da suka hada da Arak da kuma Natanz.

Hukumomin Isra'ila sun soki hare-haren Iran

Mataimakin ministan harkokin wajen Isra’ila ya ce harin da aka kai Soroka “na gangan ne” kuma “laifi ne.”

Firayim Minista Netanyahu ya ce:

“Za mu sakawa masu mulkin danniya na Tehran daidai da abin da suka aikata.”

Ministan tsaro, Katz ya kara da cewa:

“Khamenei yana bayyana burinsa na hallaka Isra’ila, shi da kansa ke ba da umarnin kai hari kan asibitoci.”

Hukumar asibiti ta ce gobara ta hallaka wasu sassa, ta fasa tagogi da rushe rufin gine-gine, wani sashe na asibitin ya lalace matuka.

Kara karanta wannan

Ukraine ta faɗi matsalar da za ta faɗa kan rikicin Isra'ila da Iran, ta kama layinta

Shugaban asibitin, Farfesa Shlomi Codish, ya ce za a mayar da marasa lafiya 200 zuwa wasu cibiyoyin.

Iran ta kai mummunan hari Isra'ila
Iran ta yi wa Isra'ila barna bayan harin makami mai linzami. Hoto: Hoto: Getty Images.
Source: Getty Images

Yadda makaman Iran ke barna a Isra'ila

A safiyar Alhamis, wani makami mai linzami daga Iran ya bugi Ramat Gan, gabashin Tel Aviv, inda gilashi da sandar lantarki suka fadi.

Hukumomi a Iran suka ce kimanin mutane 20 ne suka ji rauni a harin yankin, yayin da aka samu lalacewar gine-gine da kayan lantarki.

Rundunar Isra’ila ta gargadi mazauna garuruwan Arak da Khondab na Iran da su bar wurin, kafin farmakin da suka kai.

Sansanonin da aka kai wa farmaki sun hada da wani sinadari mai nauyi da ke cikin wani bincike da ake gudanarwa.

Rasha ta goyi bayan kasar Iran

Kun ji cewa shugabannin Rasha da China sun caccaki hare-haren Isra’ila a kan Iran, suna masu kira da a bi hanyar diflomasiyya wajen warware rikicin.

Kasar ta fitar da gargadi mai ƙarfi ga Amurka da ka da ta tsoma baki a rikicin, tana cewa hakan zai janyo mummunan rikici a fadin duniya.

Shugaban Rasha, Vladimir Putin ya nemi zama mai sasantawa tsakanin Isra’ila da Iran, bayan tattaunawa da Netanyahu da shugaban Iran.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.