Jerin jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya

Jerin jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya

  • Kamfanin BudgIT ya fitar da rahoton State of States na 2021 na jihohin da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya
  • A bisa ga rahoton, bakwai daga cikin jihohin sun kasance daga yankin arewa yayin da sauran ukun suka kasance a yankin kudu
  • Jihar Imo ita ce ta farko a wannan rukunin inda take da kaso 82.54 cikin 100 na marasa aiki

Rahoton State of States na 2021 da kamfanin BudgIT ya wallafa ya nuna rabe-raben matakin aikin yi a jihohin Najeriya.

Har ila yau, rahoton wanda aka wallafa kwanan nan ya ambaci Ofishin Kididdiga na Kasa (NBS) a matsayin tushensa.

Jerin jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya
Jerin jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya Hoto: Hope Uzodimma, Mohammed Badaru Abubakar, Governor Ahmadu Fintiri
Asali: Facebook

Legit.ng ta lissafa manyan jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a bisa rahoton.

1. Jihar Imo - 82.54%

Kara karanta wannan

Katsina: ‘Yan sanda sun kama tsohuwar ma’aikaciyar hukumar NIS bisa damfara ta N47m

2. Jihar Jigawa - 79.98%

3. Jihar Adamawa - 79.56%

4. Jihar Yobe - 74.12%

5. Jihar Cross River - 71.46%

6. Jihar Kogi - 67.78%

7. Jihar Taraba - 67.72%

8. Jihar Akwa Ibom - 67.69%

9. Jihar Borno - 67.10%

10. Jihar Kaduna - 67.00%

Jerin jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya
Jerin jihohi 10 da suka fi yawan marasa aikin yi a Najeriya Hoto: yourbudgit.com
Asali: UGC

Bakwai daga cikin jihohin da ke cikin jerin sun fito ne daga yankin arewa yayin da sauran ukun suka fito daga kudu.

Rashin Aikin Yi: Kana cikin waɗan da suka jawo Najeriya ta zama haka, Adesina ya maida ma Atiku Martani

A wani labarin, Mista Femi Adesina, mai baiwa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, ya ce tsohon shugaban ƙasa Atiku Abubakar na cikin waɗan da suka ɓata Najeriya.

Kara karanta wannan

Zangon karatu na 2021/2022: Jerin jami'o'in da suka sanar da ranakun zana jarabawar Post UTME

A martani da ya maida masa kan magan-ganun da ya yi kwanan nan, Adesina ya ce "Atiku ba zai iya tsame hannunsa daga yadda Najeria ta zama ba."

Atiku, wanda shine ɗan takarar shugaban kasa ƙarkashin jam'iyyar PDP a zaɓen 2019, ya ce a ƙarƙashin mulkin Buhari Najeriya ta kama hanyar lalacewa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel