Karin yan Boko Haram 19 sun mika wuya ga jami'an Sojoji a Borno

Karin yan Boko Haram 19 sun mika wuya ga jami'an Sojoji a Borno

  • Jami'an Sojojin Najeriya sun samu gagarumin nasara a Arewacin Najeriya
  • Hukumar ta sanar da mika wuyan wasu yan ta'addan Boko Haram da iyalinsu
  • Kakakin hukumar, Manjo Janar Onyema Nwachukwu ya bayyana hakan a jawabin da ya saki ranar Laraba

An samu sabon nasara a yaki da yan ta'adda yayinda wasu yan Boko Haram/ISWAP suka mika wuya ga rundunar FOB dake Bama, jihar Borno.

A jawabin da Diraktan yada labarai na hukumar Soji, Manjo Janar Onyema Nwachukwu, ya saki ranar Laraba, 4 ga Agusta, yace mayaka 14 tare da iyalansu suka mika wuya.

Nwachukwu ya ce Sojojin sun karbi tubabbun yan ta'addan ne a cikin dajin Sambisa ranar Lahadi, 2 ga watan Agusta.

Karin yan Boko Haram 19 sun mika wuya ga jami'an Sojoji a Borno
Karin yan Boko Haram 19 sun mika wuya ga jami'an Sojoji a Borno Hoto: HQ Nigerian Army
Asali: Facebook

Yace:

"Yan ta'addan sun hada da maza mayaka 19, mata 19 da yara 49 yan garin Njimia kuma sun ajiye makamansu."
"Yan ta'addan da iyalansu yanzu haka na hannun jami'ai don gudanar da bincike kansu, yayinda aka yiwa yaran rigakafin shan inna."

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Yan Ta'addan ISWAP Sun Mamayi Sojoji Sun Bude Musu Wuta a Borno

Shugaban Sojin kasa, Faruk Yahaya, ya jinjinawa Sojoji bisa wannan nasara da suka samu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel