TUC Ta Nemi Gwamnatin Kaduna Ta Biya Ma’aikatan da Ta Kora Hakkokinsu

TUC Ta Nemi Gwamnatin Kaduna Ta Biya Ma’aikatan da Ta Kora Hakkokinsu

- Kungiyar kwadago a jihar Kaduna ta nemi gwamnati ta biya wadanda ta kora daga aiki hakkokinsu

- Ta kuma bukaci wadanda suka yi ritaya ma a basu masu don rage radadin talauci da rashin ayyukan yi

- Hakazalika kungiyar ta karyata jita-jita da ke yawo cewa za a sallami ma'aikatan gwamnati da suka haura shekaru 50

Kungiyar kwadago reshen jihar Kaduna (TUC) ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta biya hakkokin dukkan wadanda suka yi ritaya da kuma ma’aikatan da lamarin kora ya shafa kwanan nan.

Kungiyar kwadagon ta ce biyan zai magance matsin tattalin arzikin da suke fama dashi da kuma rage radadin rashin ayyukan yi, Daily Trust ta ruwaito.

KU KARANTA: An Kama Wasu Ma’aikatan Gwamnati Daga Cikin ’Yan Bindiga a Jihar Zamfara

TUC Ta Nemi Gwamnatin Kaduna Ta Biya Ma’aikatan da Ta Kora Hakkokinsu
TUC Ta Nemi Gwamnatin Kaduna Ta Biya Ma’aikatan da Ta Kora Hakkokinsu Hoto: silverbirdtv.com
Asali: UGC

Shugaban kungiyar na jihar, Kwamared Abdullahi Danfulani da ya bayyana hakan a wani taron manema labarai don bikin ranar ma’aikata, ya ce yana da matukar ciwo a sallami mutum daga aiki ko kuma ya yi ritaya daga aiki ba tare da an biya shi hakkokinsa ba.

Danfulani, ya karyata jita-jitar da ake ta yadawa a kafafen sada zumunta na cewa gwamnatin jihar na shirin rage ma'aikata masu shekaru 50 zuwa sama daga Ma’aikatan Gwamnati.

KU KARANTA: An Tsinci Gawar Wani Yaron da Aka Sace a Magudanar Ruwa Bayan Biyan Fansa

A wani labarin, Kungiyar kwadago na kasa reshen jihar Kaduna ta alakanta rashin tsaro a jihar da korar ma'aikata da gwamnatin jihar ta yi, The Nation ta ruwaito.

Kungiyar ta ce gwamnatin Nasiru El-Rufai ta kori ma'aikata 30,000 tun bayan hawa karagar mulki a shekarar 2015.

Babban sakataren kungiyar hadaka ta AUPCTRE, Comrade Sikiru Waheed, shi ne ya bayyana haka yayin bikin ranar ma'aikata a Abuja.

Asali: Legit.ng

Online view pixel