'Yan bindiga 7 sun ajiye makamai sun mika wuya da kansu a Zamfara (Hotuna)

'Yan bindiga 7 sun ajiye makamai sun mika wuya da kansu a Zamfara (Hotuna)

- A karkashin shirin samar da zaman lafiya, yan bindiga 7 sun tuba sun mika makamai a Zamfara

- Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle ne ya karbi yan bindigar a gidan gwamnati a Gusau

- Sarakuna da wakilai daga hukumomin tsaro suma sun hallarci taron na mika makaman a Gusau

Wasu yan bindiga su bakwai sun rungumi zaman lafiya sun ajiye makamai sun mika wuya a jihar Zammfara.

Gwamnan jihar Bello Matawalle ne ya karbe su a gidan gwamnati da ke Gusau kamar yadda TVC ta ruwaito.

'Yan bindiga 7 sun ajiye makamai sun mika wuya da kansu a Zamfara (Hotuna)
'Yan bindiga 7 sun ajiye makamai sun mika wuya da kansu a Zamfara (Hotuna). Hoto: @TVCNews
Asali: Twitter

'Yan bindiga 7 sun ajiye makamai sun mika wuya da kansu a Zamfara (Hotuna)
'Yan bindiga 7 sun ajiye makamai sun mika wuya da kansu a Zamfara (Hotuna). Hoto: @TVCNews
Asali: Twitter

Tubabbin yan bindigan sun mika makamansu da suka hada da bindigu kirar AK 47, alburusai da harsasai fiye da dubu daya.

Wasu daga cikin sarakuna a jihar ta Zamfara sun hallarci taron na mika makaman da rungumar zaman lafiya.

Kazalika, wakilan hukumomin tsaro da suka hada da rundunar sojoji da wasu hukumomin sun hallarci taron.

Asali: Legit.ng

Online view pixel