Babu tabbacin gudanar da zaben kece raini a jihar Adamawa - INEC

Babu tabbacin gudanar da zaben kece raini a jihar Adamawa - INEC

Ba lallai zaben zagaye na biyu na kece raini da hukumar zabe ta kasa (INEC) ke shirin gudanarwa a jihar Aadamawa ya yiwu saboda hukuncin da ake saka ran kotu zata yanke a gobe, Alhamis.

Kwamishinan hukumar INEC a jihar Adamawa, Barista Kassim Gaidam, ya shaidawa manema labarai yau, Laraba, a Abuja cewar duk da INEC ta kammala dukkan shirye-shirye domin gudanar da zaben, hukuncin da kotun zata yi gobe shine zai tabbatar ko zaben zai yiwu ko akasin haka.

A baya kwamishinan ya bayyana cewar kotu ba ta da ikon dakatar da INEC daga gudanar da zaben kece rainin, ya na mai kafa hujja da wasu dokokin zabe.

A ranar Juma'a, 14 ga watan Maris ne, Jastis Abdul-Azeez Waziri na babbar kotun jihar Adamawa da ke Yola ya umarci INEC ta dakatar da gudanar da zaben har sai an saurari wani korafi da aka shigar kotun.

Zaben kece raini: APC da PDP na da damar samun nasara 50/50 a Adamawa - INEC
APC da PDP na da damar samun nasara 50/50 a Adamawa - INEC
Asali: UGC

Dan takarar gwamna a jam'iyyar MRDD, Eric Theman, ne ya shigar da korafi a gaban kotun bisa zargin cewar babu alamar jam'iyyar sa a jikin kuri'a.

"A matsayin mu na hukuma mai mutunta doka, zamu yi biyayya ga umarnin kotu a kan zaben da za a maimaita," a cewar kwamishinan cikin wani salo da za a iya fassara shi da mi'ara koma baya.

DUBA WANNAN: Maimaita zabe: Rundunar sojin sama ta fara jigilar kayan aiki zuwa jihohi

Ya kara da cewa INEC ta tura tawagar manyan lauyoyi daga hedikwatar ta dake Abuja domin su kare ta a karar da za a saurara a gobe.

Jam'iyyar APC da PDP na da damar samun nasara 50/50 a jihar Adamawa matukar kotu ta umarci INEC ta saka alamar jam'iyyar MRDD a jikin kuri'a kuma ta saka sabon zabe.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel