Shugaba Buhari yayi magana kan bullar faifan bidiyon hatsabibi Nnamdi Kanu

Shugaba Buhari yayi magana kan bullar faifan bidiyon hatsabibi Nnamdi Kanu

- Shugaba Buhari yayi magana kan bullar faifan bidiyon hatsabibi Nnamdi Kanu

- Yace wannan ya nuna cewa gwamnati bata kashe shi ba

- Nnamdi Kanu dai ya tsere daga Najeriya ne ta barauniyar hanya

Gwamnatin tarayyar Najeriya a karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta mayar da martani kan wani faifan bidiyo da yanzu haka yake yawo a a kafofin sadarwar zumunta na zamani dauke da muryar hatsabibin nan Nnamdi Kanu dake zaman jagoran kungiyar IPOB inda a ciki yake cewa zai dawo kasar.

Shugaba Buhari yayi magana kan bullar faifan bidiyon hatsabibi Nnamdi Kanu
Shugaba Buhari yayi magana kan bullar faifan bidiyon hatsabibi Nnamdi Kanu
Asali: Facebook

KU KARANTA: Dalilin da ya sa ba mu kaunar Shugaba Buhari - Gwamna Ortom

Mai taimakawa shugaban kasar ta fannin yada labarai na musamman, Malam Garba Shehu ne ya mayar da martanin inda yace idan har da gaske ne jagoran 'yan kungiyar IPOB da ke fafutikar kafa kasar Biafra ya yi bayani a bidiyon, to gaskiya ta fara bayyana game da zargin da ake yi mata na salwantar da shi, kuma tana dakon shigarsa kasar.

Legit.ng Hausa ta samu cewa a wani bangaren guda kuma ana ma tababa ne kan ainihin lokacin da aka dauki hotunan Kanu da ake ta yadawa cewa ya bayyana a kasar Isra'ila.

Shi dai Nnamdi Kanu a watannin baya an dena jin duriyar sa tun bayan da jami'an tsaron Najeriya suka kutsa har cikin gidan sa lokacin da yake ta fafutukar ganin an raba Najeriya.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng