‘Yan Zaria sai murna suke yi an fatattaki makarantar Shi’a

‘Yan Zaria sai murna suke yi an fatattaki makarantar Shi’a

- Mabiya Kungyar IMN ta shi’a sun saba fito-na-fito da Hukuma a Kasar nan

- Don haka Gwamnati ta haramta ayyukan ‘yan shi’a a Jihar Kaduna

- Ana tunanin Kungiyar na da goyon baya daga kasashen ketare

‘Yan Zaria sai murna suke yi an fatattaki makarantar Shi’a

 

 

 

 

 

 

Jama’a sun shiga tsalle suna murna a Garin Zaria bayan da aka rusa wata Makaranta ta Kungiyar IMN ta ‘Yan shi’a. Hukuma dai ta rusa Makarantun na Firamare da Sakandare na shi’a ne a Jiya, Alhamis.

An rusa wannan Makaranta mai suna Fudiyya da ke Babban Dodo da ke Gangaren Fadama cikin Zaria City. Gwamnatin Jihar ce dai ta bada umarni rusa wannan cibiyar Makaranta. Wannan makaranta Fudiyya ta mabiya shi’a ce.

KU KARANTA: ISIS sun kai harin bakin wake

A kwanakin baya Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya haramta ayyukan shi’a a fadin Jihar. Gwamnoni da dama kuma suka yi ta bin sahu a fadin Arewacin Kasar. ‘Yan unguwar dai sun yi tsalle da farin ciki da aka ruguza wannan makaranta, wani mazaunin wurin yace madalla, abu yayi daidai.

Shugaban Kungiyar dai ta Islamic Movement of Nigeria (IMN) yana nan a tsare tun shekar bara. Kwanan an kara samun wata takkadama tsakanin ‘Yan Shi’a da ‘Yan Sanda a Garin Kano.

A biyo mu a shafin mu na Tuwita @naijcomhausa

https://youtu.be/wXmmTEAKDxo

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng