Babu Ahmed Musa a Jerin 'Yan Wasan Najeriya 55 da Za Su Iya Buga Gasar AFCON

Babu Ahmed Musa a Jerin 'Yan Wasan Najeriya 55 da Za Su Iya Buga Gasar AFCON

  • Kocin Super Eagles, Eric Chelle ya fitar da jerin ƴan wasa 54 da ke da damar wakiltar Najeriya a gasar AFCON ta 2025/2026
  • Jerin ya hada da ’yan wasa da ke taka leda a waje da kuma wasu daga NPFL, inda a cikinsu za a zaɓi 28 da suka fi cancanta
  • Sai dai, a gaba daya jerin ƴan wasa 54 da Chelle ya fitar, ba a ga sunan tsohon kyaftin din Super Eagles, Ahmed Musa ba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Kocin Super Eagles, Eric Chelle ya fitar da jerin ƴan wasa 54 da ke da damar wakiltar Najeriya a gasar AFCON cikin wannan wata, inda daga bisani za a zaɓi 28 da suka fi cancanta.

Sai dai, a gaba daya jerin ƴan wasa 54 da aka fitar, ba a ga sunan fitaccen dan wasan kungiyar, kuma tsohon kyaftin dinta, Ahmed Musa ba.

Kara karanta wannan

Wani bam ya tarwatse da mutane a Banki, an samu asarar rayuka a jihar Borno

Kocin Super Eagles ya fitar da sunayen 'yan wasan da za su taka leda a gasar AFCON 2025/2026
Kocin Super Eagles, Eric Chelle bai sanya sunan Ahmed Musa a 'yan wasan AFCON ba. Hoto: @NGSuperEagles
Source: Getty Images

An fitar da tawagar Super Eagles da za ta AFCON

Ahmed Musa ya wakilci Super Eagles sau hudu a gasar, duk da cewa bai buga ko wasa ɗaya ba a gasar ta 2023, in ji wani rahoton BBC Hausa.

Fitattun ’yan wasan Najeriya da suka yi fice a wasanni na duniya sun samu gurbi a cikin jerin da aka fitar a ranar Talata, 02 ga Disamba 2025.

'Yan wasan da suka shiga jerin sun hada da kyaftin William Troost-Ekong, Victor Osimhen, Wilfred Ndidi, Stanley Nwabali da Maduka Okoye.

Sauran sun hada da Calvin Bassey, Zaidu Sanusi, Semi Ajayi, Frank Onyeka, Alex Iwobi, Raphael Onyedika, Ademola Lookman, Simon Moses, Samuel Chukwueze da Chidera Ejuke.

AFCON: Chelle ya bai wa ’yan NPFL dama

Kocin ya kuma fadada binciken sa ta hanyar kiran ’yan wasan cikin gida irin su Abdulrasheed Shehu, Ebenezer Harcourt, Ekeson Okorie, Chisom Orji da Adekunle Adeleke.

Kara karanta wannan

Sheikh Gumi ya yi zazzafar addu'a kan 'yan ta'adda da masu taimakonsu

Wannan mataki ya fayyace cewa yana son ganin kwarewar 'yan wasan da ke buga wasannin kofin NPFL, da kuma tantance kwarewarsu kafin ya kammala zabin karshe na ’yan wasa 28.

Shi ma Musa wanda ya taka leda a Turai yanzu yana buga wasa ne a kungiyar Kano Pillars.

Super Eagles za su bude sansanin atisaye a Masar ranar 10 ga Disamba, 2025 inda za su buga wasannin gwaji, a cewar rahoton Channels TV.

An saki sunayen 'yan wasan da za su buga wa Najeriya a AFCON 2025/2026
'Yan wasan Super Eagles sun yi shirin fafata wasa. Hoto: @NGSuperEagles
Source: Getty Images

Super Eagles da jadawalin AFCON 2025

Jerin da aka fitar ya kunshi masu tsaron gida shida, masu tsaron baya 13, ’yan wasan tsakiya wasa 12, sannan kuma akwai 'yan wasan gaba 23.

Ebenezer Akinsanmiro na Inter Milan, wanda yake wasa a Pisa yanzu, ya samu gurbi a jerin wucin-gadi, kuma ana sa ran zai shiga jerin karshe.

Najeriya za ta fitar da jerin ’yan wasa 28 a ranar 11 ga Disamba, 2025 ko kafin wannan lokaci, domin za a fara buga wasan AFCON din ne daga 21 ga Disamba 2025 zuwa 18 ga Janairu 2026.

Super Eagles za su fafata da Tanzania, Uganda da Tunisia a rukuni na C, a cewar rahotannin da aka samu.

Kara karanta wannan

Kasa ta rikice: 'Yan bindiga sun yi garkuwa da kusa a APC

Masu sharhi sun yi martani

A zantawar Legit Hausa da mai sharhi kan lamuran wasanni, Saminu Adamu Namunaye daga Globe FM Bauchi, ya ce ba abin mamaki ba ne don an ga babu sunan Ahmed Musa a wannan jadawalin.

Saminu Namunaye ya ce:

"Babu shakka Ahmed Musa ya taka gagarumar rawa a tawagar Super Eagles a tsawon shekarun da ya shafe yana taka masu leda a baya.
"A lokacin da yake kan ganiyarsa, ya kasance ɗan wasa mai gudu, ƙarfin zura kwallaye, ya kawo nasarori masu yawa a baya. Ya zama dan Najeriya na farko da ya zura kwallaye fiye da sau ɗaya a Kofin Duniya, wannan babban tarihi ne.
"Ya cancanci yabo da godiya saboda kwarewar da ya nuna a baya, amma ƙwallon ƙafa na da lokaci, kuma dole ne Eric Chelle ya yi amfani da ƴan wasan da ke kan ganiyarsu don cimma nasara."

Namunaye ya ce yanzu haka ma Ahmed Musa ba shi da wadataccen lokacin buga kwallo, don ya mayar da hankali kan inganta tawagar Kano Pillars.

Kara karanta wannan

CBN ya kawo sabuwar doka kan ajiya da cire kudi a Najeriya, za ta fara aiki a 2026

Amma ya ce har yanzu Super Eagles tana bukatar shawarwari daga ƴan wasan da suka ƙware irin Ahmed Musa, wanda ya ce yana da kyakkyawar alaka da ƴan wasa, saboda ya taba riƙe Kyaftin ɗin kungiyar.

Ahmed Musa ya raba motoci a Kano Pillars?

A wani labarin, mun ruwaito cewa, dan wasan Super Eagles, Ahmed Musa, ya yi martani kan rahoton cewa ya raba motoci ga yan Kano Pillars.

Ahmed Musa ya karyata rade-radin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa ya bai wa ’yan wasan Kano Pillars da jami’ai motoci masu tsada.

Soshiyal midiya ta kaure da labarin cewa Musa ya bai wa kowane ɗan wasa da jami’in koyarwa sababbin motoci kirar 'Land Cruiser' domin bikin dawowarsa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com