Siyasar Najeriya
Hon.Ahmed Mirwa Lawan ya rasa kujerarsa, kakakin majalisar dokokin jihar Yobe ya sha kaye hannun dan shekara 35, shima kakakin majalisar Filato ya sha kaye.
Yayin da sakamakon zabe ke ci gaba da fitowa daga sassan jihar Kano, NNPP ta fara lashe zaben majalisar dokokin Kano, inda Falgore ya samu nasara a mazaba Rogo.
‘Yan Bindiga sun kashe wani Shugaban yakin neman zaben APC da suka yi garkuwa da shi. Ana tunanin Chisom Lennard ya rasu ne yana hana ‘yan daba yin magudi.
Sanata Aishatu Ahmed Binani, yar takarar gwamnan jihar Adamawa karkashin inuwar APC, ta ce kuri'u na wurin mata a yanzun, idan suka zabe ta zata samu nasara.
A wannan zaben, jam'iyyar PDP ta samu nasarar samun kujerar farko ta majalisar dokokin jiha bayan da ta lallasa dan takarar jam'iyyar APC a jihar da ke Arewa.
Rahoto ya nuna cewa jami'an tsaro sun bindige tsohon kansila na gundunar Getso a jihar Kano, Ibrahim Nakuzama, kan satar akwatin zabe, na kusa dashi ya tabbatar
Rahoton da muke samu daga jihar Neja ya bayyana yadda 'yan siyasa ke sayen kuri'un talakawa da taliya da sauran kayan abinci a bangarori daban-daban na jihar.
Jami'an hukumar EFCC sun sha dakyar a hannun 'yan daba a jihar Kaduna a lokacin da suka zo kama wani da ake zargin yana saen kuri'un jama'a a wurin zaben nan.
Hyacinth Alia, dan takarar jam'iyyar gwamna na Jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a Benue ya lallasa takwararsa na PDP a akwatunan zaben gidan gwamnati.
Siyasar Najeriya
Samu kari