Jihar Ondo
Majalisar dokokin jihar Ondo ta yi sauye-sauye don ɗinke eɓaraka a tsakanin shugabanninta, mataimakin kakaki da shugaban marasa rinjaye sun hakura da kujerunsu.
Wasu masu zuwa coci ɗaukar karatun Littafi Mai Tsarki (Bible) sun faɗa hannun ƴan bindiga a hanyarsu ta komawa gida a Akure ta Yamma a jihar Ondo.
Rahotanni sun tabbatar da cewa yan bindiga da suka sace shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Ose a Ondo, Nelson Adepoyigi sun hallaka shi da gangan.
Wata kotu a jihar Ondo ta gurfanar da wani basarake kan zargin cin zarafin mutanensa. Sarkin ya yi wa wasu mutane bulala kan gaza biyan harajin da ya daura musu.
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun daure mutane 2 da suka je daji karbo shugaban APC da aka yi garkuwa da shi. Mutanen sun kai kudin fansa amma aka rike su.
Wasu mahara da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun sace shugaban APC na gunduma ta 5 Ifon a ƙaramar hukumar Ose ta jihar Ondo, sun nemi fansar N100m.
Tsohon dan takarar gwamna na NNPP a Ondo, Hon. Olugbenga Edema, ya fice daga jam’iyyar saboda rashin gaskiya da rikice-rikicen cikin gida da cin amana.
Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya ba mutane da dama mamaki a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa, ya shiga aji ya koyar da ɗalibai a wata makaranta a jihar Ondo.
Gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa ya samu nasarar a ƙarar da NNPP da ɗan takararta na gwamna, Hon. Gbenga Edema suka kalubalanci zaɓen fidda gwanin APC.
Jihar Ondo
Samu kari