Sarkin Kano
Majalisar jihar Kano ta gabatar da kudirin samar da sarakuna guda uku masu girman daraja ta biyu da za su ƙasa ƙarƙashin Sarki Muhammadu Sanusi II.
Sarkin Dawaki Babba, Baffa Dan Agundi ya bayyana kuskuren da aka yi tun farko kan mayar da Sanusi II sarauta inda ya ce shi ba ɗan sarki ba ne domin gadonta ake yi.
Bayan yanke hukunci kan dambarwar sarauta, Kungiyar Kano Democratic Vanguard ta ce hukuncin abin kunya ne ga bangaren shari'a ganin yadda aka nuna son kai a fili.
Babbar kotun jihar Kano ta umarci sarakuna 5 da aka tsige a Kano su mayar da kayan sarautar da ke hannunsu ga Gwamnatin jihar ko Sarki na 16 Muhammadu Sanusi.
Babbar kotun jiha da ke zamanta a Kano ta kawo karshen rikicin masarautar Kano, ta yanke hukunci a yau Litinin na haramtawa Sarki Ado Bayero bayyana kansa da sarki.
Gamayyar kungiyoyin matasan Kano (KYC) ta yi ikirarin cewa gobarar da ta tashi a fadar Sarkin Kano Sanusi II ya nuna cewa ubangiji bai ji dadin dawo da shi ba.
Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso ya ce Gwamna Abba Kabir na jihar Kano ya dauki matakin rushe masarautu saboda cika alkawuran kamfe da ya dauka.
Ana fargabar gobara ta jawo asara mai tarin yawa a fadar Sarkin Kano bayan iftila'in da ya faru a daren jiya Juma'a 12 ga watan Yuli 2024 a fadar da ke Kofar Kudu.
Wasu fusatattun mazauna masarautar Rano a jihar Kano sun kori wakilin da Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya tura zuwa masarautar da aka rushe.
Sarkin Kano
Samu kari