Hukumar Sojin Najeriya
Hedikwatar rundunar tsaro (DHQ) ta sanar da cewa dakarun sojoji sun sheke yan ta'adda 6,886 da cafke 6,970 da ake zargi daga watan Janairu zuwa Disamban 2023.
Dakarun sojin Najeriya sun ikirarin cewa sun dakile yunkurin yan bindiga na shiga kauyuka 19 a kananan hukumomin Bokkos da Barkin Ladi a jihar Filato ran jajibiri.
Wani jami'in hukumar NSCDC, Abubakar Nurudeen, ya rasa ransa sakamakon taka wani abun fashewa bisa tsautsayi a jihar Borno ranar Alhamis da ta gabata.
Rahotanni sun bayyana cewa tsagerun yan bindiga sun kashe yan sanda biyu yayin da suka farmaki ayarin jagoran PDP a jihar Anambra, Chris Uba jiya Alhamis.
Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle ya gargadi sabbin Burgediya Janar 47 da suka samu karin girma zuwa Manjo Janar kan dakile matsalar tsaro a Najeriya.
Yayin da ake ci gaba da alhinin kisam bayin Allah 195 a kananan hukumomi uku a jihar Filato, wasu miyagu sun sake kai sabon hari wani kauye jiya da daddare.
Wasu tsagerun yan bindiga sun kashe rayukan mutane akalla 16 a sabon harin da aka tabbatar sun kai wani kauye a jihar Filato, gwamna ya yi Allah-wadai.
Rundunar sojojin Najeriya ta yi wa ofisoshinta 112 karin girma zuwa mukamin janar. Hakan na zuwa ne bayan rundunar ta yi wa wasu manyan sojojin murabus a baya-baya.
Rundunar sojin Najeriya ta yi nasarar kwato mutane 52 daga sansanin 'yan bindiga a karamar hukumar Isa da ke jihar Sokoto a jiya Juma'a 22 ga watan Disamba.
Hukumar Sojin Najeriya
Samu kari