Hukumar yan sandan NAjeriya
Rundunar 'yan sandan jihar Imo ta kama mutane 3 dauke da kokon kan dan Adam domin yin tsafi. Mutanen sun ce wani ne ya ba su wanda an bazama nemansa.
Rundunar 'yan sanda a jihar Bauchi ta kai farmaki maboyar 'yan ta'adda a Alkaleri inda ta yi jina jina ga 'yan ta'addar da kashe wasu biyu da kwato makamai.
Rundunar 'yan sanda ta kama bakin haure 165 da suka shigo Najeriya daga kasashen waje domin damfara a Najeriya. An kama mutanen a Kebbi kan barazanar tsaro.
An kashe jami’an tsaro 326 a Najeriya cikin shekara guda. Ƴan sanda 258, sojoji 59 sun mutu yayin da su ma NSCDC da hukumar shige da fice suka rasa jami’ansu.
ACP Dauda Fika, jarumin dan sanda da ke yaki da Boko Haram, ya rasu a Abuja. Ya jagoranci hare-haren kwato garuruwa a Yobe da Borno daga hannun ‘yan ta’adda.
Rundunar ƴan sandan jihar Ogun ta gurfanar da wani dattijo a gabam kuliya kan tuhumar haɗin kai, cin zarafin wani bawan Allah, kotu ta ɗage zaman.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun tare matafiya a jihar Ondo. 'Yan bindigan sun sace fasinjoji masu yawa tare da tursasa su zuwa cikin daji.
Bayan zargin cin zarafi da wani basarake ya yi, Gwamnatin jihar Ogun ta dakatar da Oba Abdulsemiu Ogunjobi na Orile Ifo na tsawon watanni shida daga sarauta.
Babbar kotun jihar Kano ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya kan wasu mutum 5 da ake tuhuma da kashr mata a yankin ƙaramat hukumar Wudil ta Kano.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari