Hukumar yan sandan NAjeriya
A labarin nan, za a ji cewa rikice-rikicen da su ka dabaibaye sassa daban-daban a jihar Filato sun jawo asarar rayukan jama'a da su ka tasamma 12,000.
Rundunar yan sanda da ke Lagos ta ce ta wanke babban Faston House on the Rock, Fasto Paul Adefarasin, bayan bidiyon bindiga ya bazu wanda ya tayar da kura.
Gwamnatin Imo ta yi alƙawarin ceto tsohon ɗan majalisar jihar, Ngozi Ogbu, wanda wasu mayaka masu fafutukar kafa Biyafara suka sace shi, tare barazanar kashe shi.
Kungiyar KADA da ke karamar hukumar Kanam a jihar Filato ta tabbatar da cewa yan bindiga sun kashe Sarkin Shuwaka, Malam Hudu Barau bayan sace shi.
‘Yan sandan Ondo sun kama Abdullahi Saliu da ya sa dade yana sojan gona da kanal din soja ya na damfarar mutane kudi. Yanzu haka dai an gurfanar da shi a kotu.
Rahotanni sun tabbatar da mana cewa matashin da ake zargi da kisan budurwarsa a jihar Taraba ya mutu inda aka tsinci gawarsa ana tsaka da bincike kan lamarin.
Tawagar 'yan Majalisar Tarayya daga Kebbi ta bukaci hukumomin tsaro su binciki tsohon Antoni Janar, Abubakar Malami kan zarge-zargen da ya yiwa Gwamna Nasir Idris.
Yan bindiga sun shiga kauyuka biyu a kananan hukumomin Makarfi da Kudan da ke jihar Kaduna, sun yi garkuwa da wani dan siyasa da ya yi fice a yankin.
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin Mai Mala Buni ta jihar Yobe ta bayyana takaicin yadda aka dawo da labarin kisan mutum 84 a Mafa a matsayin wanda ya faru yanzu.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari