Labaran garkuwa da mutane
An bayyana yadda tsagerun 'yan bindiga suka sako dalibai mata da suka sace a jihar Zamfara. An ruwaito cewa, sun sako su ne bayan shafe wata tara a tsare.
Dakarun ƴan sanda sun damƙe wata mace da ake zargin ta yi garkuwa da kanta da kuma wasu mutane sama da 50 bisa zargin aikata manyan laifuka a Akwa Ibom.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta biya ko sisi ba a matsayin kudin fansa na daliban da 'yan bindiga suka sace a Kaduna.
'Yan bindiga sun yi awon gaba da mutane akalla 61 a wani sabon hari da suka kai garin Buda da ke karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna. Yan sanda ba su ce uffan ba.
Miyagun ƴan bindiga sun buƙaci yan uwan da mutanen da suka sace a Gonin Gora su haɗa Naira tiriliyan 40 a matsayin kuɗin fansa da kuma motoci da babura.
Masu garkuwa da mutane da suka sace almajirai a jihar Sakkwato sun nemi a tattara musu Naira miliyan 20 a matsayin kuɗin fansa gabanin su sako su.
Wasu ƴan bindiga da ake zaton masu garkuwa da mutane ne sun yi awon gaba da mataimakiyar darakta da wani jami'in tsaro a asibitin jami'ar Najeriya da ke Enugu.
Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bayyana cewa ƴan bindiga na kulle-kulle kai hare-hare a makarantun wasu jihohi 14, ta ce an fara ɗaukar matakan kariya.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya nuna damuwa bisa waɗannan hare-hare na garkuwa da mutane da aka kai jihohin Borno da Kaduna.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari