Labaran garkuwa da mutane
Bishof Mathew Kukah, babban malamin cocin katolika a jihar Sakkwato ya dira kan wasu manyan ƴan Najeriya da ke haɗa kai da ƴan bindiga masu satar dalibai.
Wani shafin yanazar gizo mai tsage gaskiya ya tabbatar da cewa ikirarin cewa an yi awon gaba da mai ɗakin Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas ba gaskiya bane.
Farfesa Babagana Umaru Zulum ya ce shirin aminci a makarantu da suka kaddamar a Borno tun shekaru bakwai zuwa takwas da suka wuce yana aiki yadda ya kamata.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya koka kan yawaitar ayyukan masu garkuwa da mutane. Ya bayyana su a matsayin 'yan ta'adda wadanda za a kawo karshensu.
Wasu maharan sun yi garkuwa da matan aure 12 da namiji ɗaya, sun kwashi dukiyar bayin Allah mai ɗumbin yawa a karamar hukumar Dutsinma a jihar Katsina.
Wani ɗan bindiga ya bude shafi a dandalin TikTok, inda ya ke baje kolin irin maƙudan kuɗaɗe da makaman da tawagarsa ta tara. Lamarin da ya jawo cece-kuce.
Rahotanni sun nuna cewa wasu gungun ƴan bindiga sun halaka dakaru 2 na rundunar CPG ta jihar Zamfara tare da ƙona motoci biyu a ƙaramar hukumar Tsafe.
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya bayyana cewa kace-nace da ake ta yi kan zargin an biya kuɗin fansa wajen ceto ɗaliban Kuriga ba shi da muhimmanci.
Wata ƙungiyar matasa RUN ta bukaci hedkwatar tsaron Najeriya ta sanya suɓan Sheikh Ahmad Gumi a cikin waɗaɓda za ta kama kan zargin hannu a ta'addanci a Najeriya.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari