Labaran garkuwa da mutane
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa akwai bukatar jami'an tsaro su mayar da hankali wajen kokarin sanya ido kan al'amuran tsaro domin wanzuwar zaman lafiya.
Matasa a jihar Plateau sun yi halin maza sun cafke dan bindiga mai garkuwa da mutane bayan ya sace yara biyu. Ya karbi kudin fansa yana kokarin guduwa aka kama shi.
Daruruwan mutane sun yi sallar janzar sarkin Gobir, Alhaji Isa Muhammad Bawa a fadarsa da ke Sabon Birni a jihar Sokoto bayan yan bindiga sun hana gawarsa.
Gwamnatin jihar Enugu ta samu nasarar rusa wasu kangwayen gine gine da ake zargin masu garkuwa na amfani da su, ta kwsto miyagun makamai a wurin.
Ministan lafiya, Farfesa Muhammad Pate ya tura sako ga Nuhu Ribadu da sufeton yan sanda IGP Kayode Egbetokun kan kubutar da Dr Ganiyat Papoola daga yan bindiga.
Jama'a na nuna damuwa bayan dalibai likitoci 20 da aka sace a Benue sun yi mako daya a hannun masu garkuwa da mutane, an bukaci N50m kudin fansa.
Rahotanni daga jihar Sakkwato sun tabbatar da cewa ƴan bindiga sun sako ɗan marigayi Sarkin Gobir wa da suka sace su tare bayan basaraken ya rasu a hannunsu.
Gwamna Dauda Lawal ya musanta naɗa wanda ake zargi da hannu a ayyukan ta'addancin ƴan bindiga, Bashir Haɗeija a wani muƙamin gwamnatin jihar Zamfara.
Yan bindiga sun kashe Sarkin Gobir Isa Muhammad Bawa bayan sun yi garkuwa da shi. Mun tattaro muku tarihin sarkin Gobir da tarihin masarautar Gobir da Gobirawa.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari