Yan bindiga
Rundunar 'yan sanda a birnin tarayya Abuja ta kama wani mutum da ake zargi da cewa zai saye harsashi ya mika wa 'yan ta'adda a jihar Zamfara daga Abuja.
Sheikh Ahmad Gumi ya kare matsayinsa kan tattaunawa da ’yan bindiga, yana mai cewa babu wata dokar addini ko ka’ida ta duniya da ta haramta yin sulhu da miyagun.
Sheikh Ahmad Gumi ya jaddada cewa sace dalibai ba ya kai kashe sojoji muni, yana mai cewa dole a shiga tattaunawa da ’yan bindiga domin samun zaman lafiya.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun sake kai hari a jihar Kano. 'Yan bindigan sun yi awon gaba da wani dattijo tare da raunata dansa a harin da suka kai.
Daliban da aka ceto daga hannun 'yan bindiga a jihar Neja sun bayyana halin da suka shiga. Sun bayyana cewa 'yan bindigan sun rika yi musu barazana.
Bello Matawalle ya ce masu sukarsa na yada karya ne saboda siyasa, ya bayyana cewa ya gaji matsalar tsaro tun kafin gwamnatinsa ta ɗauki matakan magance ta.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna farin cikinsa kan ceto daliban da aka sace a jihar Neja. Ya bukaci jami'an tsaro su kubutar da sauran da ke tsare.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar ragargazar 'yan bindiga a jihar Sokoto. Sojojin sun hallaka 'yan bindiga da dama bayan sun gwabza fada.
‘Yan bindiga sun kashe matar faston Anglican a Lilu, Ihiala, sun kona gidansa da motocin cocin yayin wani mummunan hari da ya tayar da hankula a Anambra.
Yan bindiga
Samu kari