Yan bindiga
'Yan bindiga sun kashe mutane 50 a Tungan Dutse, da ke jihar Zamfara. Mazauna yankin sun ce an yi watsi da gargaɗin su kafin harin ya auku a cikin watan Ramadan.
'Yan ta’adda sun tura wasika ga al’ummar Utono, Kebbi, suna neman N100m kafin su shiga gari domin “wa’azi”, yayin da gwamnati ta tura jami’an tsaro don kare su.
'Yan ta'addan kungiyar Lakurawa sun kai wani harin ta'addanci a jihar Kebbi. Tsagerun 'yan ta'addan sun kashe mutane tare kuma da yi awon gaba da shanun bayin Allah.
Gani Adams ya gargaɗi gwamnati kan shirin ƴan ta'adda na kai hari a Ira, Inaja da Aho a Kwara, bayan an tsinci wasiƙar barazana da miyagun suka ajiye a kasuwa.
Mahara sun kashe Oba Kehinde Jacob Falodun na Agamo a Ondo. Yan sanda da Amotekun sun fara bincike bayan an tsinci gawar sarkin da raunukan bindiga.
Gwamnatin jihar Zamfara ta ba jami'an tsaro motocin yaki masu sulke da jiragen yaki marasa matuka domin yakar 'yan bindiga. Ministan tsaro ya halarci taron.
Rundunar 'yan sanda reshen jihar Kaduna ta samu nasarar hallaka yan bindiga da dama tare da kama wasu mamyan jagorori 17 a kananan hukumomi hudu.
Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi Allah-wadai da harin ta’addanci a Kwara. An sa ran hukunta masu hannu da harin da ya kashe sama da mutane 160.
Wani dan bindiga ya kai hari filin wasa bayan jama'a sun taru a kasar Amurka. 'yan sanda sun tabbatar da cewa mutane uku sun mutu a harin wasu kuma na asibiti.
Yan bindiga
Samu kari