Jihar Borno
'Yan ta'addan Arewa maso Gabas sun gamu da tsaiko yayin da aka farmake su da kuma lalata motocin bindigarsu da suke shirin aikata barna a jihar Borno.
Ƴan ta'addan Boko Haram sun dasa bam a jihar Borno wanda ya yi sanadiyyar salwantar da rayukan wasu manyan kwamandojin CJTF guda biyu da wasu mutum huɗu.
Hukumar 'yan sanda a jihar Borno, sun karyata jita-jitar da ake yada wa a Maiduguri na cewar ana sace wa maza mazakuta da zaran sun yi musabaha da bakon fuska.
Akalla manoma tara ne rahotanni suka bayyana sun rasa rayukansu a wani harin boko Haram a Borno. Shekaru kenan garin Zabarmari ke fuskantar hare-haren Boko Haram.
'Yan ta'addan Boko Haram sun kai mummunan hari a gonar wani ɗan kasuwa a jihar Borno, inda suka halaka shi tare da sace manoma mutum huɗu masu aiki a gonar.
Dakarun sojojin saman Najeriya sun samu nasarar halaka ƴan ta'adda masu yawa a wasu hare-haren da suka kai a yankunan Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.
Majalisar dokokin tarayya sun mika kuka ga shugaban kasa Bola Tinubu kan yadda Giwaye daga Kamaru ke shiga jihar Borno suna lalata amfanin gona a kowacce shekara.
Luguden wutan jirgin yaƙin sojin Najeriya na rundunar Operation Haɗi Kai ya yi sanadin mutuwar mayakan Boko Haram sama da 160 a jihohin Yobe da Borno.
Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da nasarar Sanata Muhammed Ali Ndume.da Kaka Lawal na Borno ta kudu da Borno ta tsakiya, ta kori ƙarar jam'iyyar PDP.
Jihar Borno
Samu kari