Jihar Borno
Rundunar sojojin Najeriya ta tabbatar da cewa jami'anta sun hallaka 'yan ta'adda mutum shida a jihar Borno. An kashe su ne bayan sun yi wa sojoji kwanton bauna.
An sake shiga jimami bayan 'yan ta'addan Boko Haram sun yi wa sojojin Najeriya kwanton bauna a jihar Borno. Sun hallaka sojoji shida a yayin harin.
Rundunar 'yan sandan jihar Borno, ta sanar da samun nasarar cafke wasu mutum hudu da ake zargi da yunkurin kona wani sansanin 'yan gudun hijira a jihar.
An samu tashin wata mummunar gobara a kasuwar Gamboru da ke cikin birnin Maiduguri na jihar Borno. Jami'an 'yan kwana-kwana sun yi nasarar kashe ta.
Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya tura sakon jaje bayan rasuwar tsohon shugaban kungiyar NLC, Ali Chiroma a jiya Talata 2 ga watan Afrilu.
Kwamared Ali Chiroma, tsohon shugaban ƙungiyar kwadago ta ƙasa NLC ya rasu a asibitin koyarwa na jami'ar Maiduguri da ke jihar Borno ranar Talata.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu tsageru sun halaka malamin jami'ar tarayya da ke Maiduguri UNIMAID, Dakta Kamal Abdulƙadir, a ofishinsa ranar Lahadi.
Wani babban kwamandan Boko Haram kuma hatsabibin da ya hana mutane zaman lafiya a kewayen Gwoza, Mallam Yathbalwe, ya fito da kansa ya miƙa wuya.
Hedikwatar tsaro ta ce ta mika mutane 313 da ta kama ga gwamnatin Borno bisa umarnin babbar kotun tarayya da ke zamanta a Maiduguri. An gane mutanen ba su da laifi.
Jihar Borno
Samu kari