
Arewa







Mai martaba Sarkin Ningi, Alhaji Yunusa Muhammadu Danyaya, ya ce ba zai lamurci masu unguwanni su haɗa baki da vara gurbi ana hana jama'a zaman lafiya ba.

Kungiyar Kiristoci ta CAN reshen Arewacin Najeriya ta koka kan tsarin ba da tallafi na Tinubu, ta bukaci ya samar da tsari mai dorewa don rage talauci a kasa.

Rundunar 'yan sanda a jihar Kano sun haramta hawan angonci da kilisa da kuma taron majalisi don dakile matsalar tsaro da ake samu a birnin Kano baki daya.

Jam'iyyar PDP mai adawa a jihar Kebbi ta zargi gwamnan jihar, Kwamred Nasir Idris kan salwantar da makudan kudade har Naira biliyan 20 cikin kwanaki dari kacal.

Gwamnatin Adamawa ta kare kanta dangane da matakin sanya hoton gwamna Ahmadu Finfiri a jikin buhunan shinkafar tallafin rage zafin cire tallafin man fetur.

Allah ya yi wa shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Giro Argungu rasuwa a yau Laraba 6 ga watan Satumba bayan fama da gajeriyar jinya a Birnin Kebbi.

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya amince a tura wa kungiyar kwadago NLC reshen jihar Niger manyan Tireloli na Buhunan Shinkafa a matsayin tallafin rage radaɗi.

Kungiyar Kwadago ta Najeriya, NLC reshen jihar Neja ta ki amincewa da tsarin Gwamna Umar Bago na ware ma'aikata a cikin tsarin rabon kayan tallafi a jihar.

Bidiyon wata akuya da ta haifi ɗa mai kama da halittar jikin ɗan Adam a jihar Kwara ya ɗauki hankulan jama'a. An yaɗa bidiyon sosai a kafafen sada zumunta inda.
Arewa
Samu kari