Arewa
Rahotanni da muke samu sun tabbatar da cewa yara tara daga cikin 102 da kungiyar Boko Haram ta sace sun kubuta daga hannun ‘yan ta’adda a jihar Borno.
Allah ya yi wa Alhaji Muhammad Egba Enagi rasuwa, m5arigayin shi ne mahaifin matar gwamnan jihar Neja, Fatima Bago wanda ya riga mu gidan gaskiya da shekaru 90.
Farfesa Ibrahim Muazzam, tsohon shugaban Hisbah ya bayyana yadda 'yan siyasa suka yi kokarin kawo rudani tsakanin hukumar da gwamnatin jihar kan ayyukan hukumar.
Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana wasu larura da za su iya sanya musulmi ajiye Azumin watan Ramadana. Ya kuma fayyace wadanda zasu biya ko sabanin haka.
Gwamnan jihar Kebbi, Kwamred Nasir Idris ya sanar da shirin fara rabon kayan abinci domin rage radadi a jihar yayin da ake cikin wani mawuyacin hali a Najeriya.
Babbar kotu da ke jihar Kano ta dauki mataki kan gwamnatin jihar da majalisa inda ta dakatar da su kan gyaran fuska a dokokin wasu hukumomi guda uku.
Yan fashi da makami sun farmaki ofishin ƴan sanda da bankunan kasuwanci biyu a jihar Kogi, sun yi awon gaba da maƙudan kudade da ba a tantance ba har yanzu.
Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya ya bai wa daliba Hajara Ibrahim Dan'azumi kyautar naira miliyan biyar inda hukumar Alhazai ta ba ta kyautar kujerar hajji.
Majalisar jihar Jigawa ta tsige wasu daga cikin manyan masu mukamai a Majalisar da kuma ciyamomi guda hudu a jihar kan zargin hadin baki da cin amana.
Arewa
Samu kari