Majalisar dokokin tarayya
Kungiyar dattawan Zamfara ta nuna damuwa kan ci gaba da muzgunawa wasu daga cikin zababbun 'yan majalisar dokokin jihar. Ta ja kunnen Gwamna Dauda Lawal.
Rahoton hukumar kula da albashi na 2007 ya nuna cewa shugabannin kasa na samun fiye da Naira miliyan 10 a kowace shekara, alawus din mazaba kadai na kai N8m.
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta ce ba za ta janye karar da ta shigar kan Godswill Akpabio ba, yayin da a hannu daya wasu ke zarginta da siyasantar da lamarin.
Hon. Mike Dio Jen ya yi murabus daga kujerar ɗan Majalisar dokokin jihar Taraba domin karɓar muƙamin kwamishina da Gwamna Agbu Kefas ya naɗa shi.
Kotun daukaka kara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa Farfesa Peter Ogban kan magudin zabe da ya yi don Godswill Akpabio bisa canja sakamako.
Tsohon Sanata, Bala Ibn Na’Allah, ya bayyana irin kalubalen da wasu ‘yan majalisar Najeriya ke fuskanta bayan sun bar kujerunsu. Ya ce ba sa iya biyan bukatunsu.
Sarakunan gargajiya daga yankin Kudu maso Gabas sun sha alwashin ba wa Shugaba Tinubu 70% na kuri’un yankin, tare da yi masa addu’ar samun albarka.
Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio ya ce talauci ba laifi ba ne, yana kiran ‘yan Najeriya da su rungumi juna da raba abin da suka mallaka.
Dan majalisa mai wakiltar Bichi a majalisar wakilai, Hon Abubakar Kabir Bichi zai dauki nauyin dalibai mata 'yan asalin karamar hukumar domin karo karatu.
Majalisar dokokin tarayya
Samu kari