Yan ta'adda
Hedkwatar tsaro ta sanar da gagarumin nasara da dakarun soji suka samu a ayyukan da suka gudanar a fadin kasar cikin mako guda. Sun hallaka 'yan ta'adda 185.
Wani dan sanda ya gamu da ajalinsa a ranar Alhamis a jihar Ebonyi lokacin da wasu ‘yan bindiga suka bude wuta kan tawagar ‘yan sanda da ke sintiri.
Lamarin rashin tsaro yana cigaba da zama abin ban tsoro bayan kashe Sarki. Olukoro na kasar Koro ya riga mu gidan gaskiya a sakamakon hari da aka kai har cikin fada.
Yunkurin kawo karshen ta'addanci da tsagerancin 'yan bindiga ya yi nisa. Gwamnatin Najeriya ta saye jiragen AH-1Z da kayan yaki daga hannun Amurka.
Sanata mai wakiltar mazabar Delta ta Arewa, Ned Nwoko, ya yi magana game da ba ‘yan Najeriya damar mallakar bindiga don kare kansu daga harin 'yan bindiga.
Wasu ‘yan bindiga a ranar Laraba sun kai hari a kauyukan Akinde, Tse Yongo, Tse Adem da Tse Ahikyegh a karamar hukumar Donga a jihar Taraba, sun kashe mutum uku.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da sabuwar rundunar tsaro wacce za ta yi fito na fito da ƴan bindigan da suka daɗe suna addabar jihar.
Wani bam da ƴan ta'addan Boko Haram suka dasa ya tashi da wasu mutane a jihar Borno. Bam ɗin dai ya yi sanadiyyar halaka mutum 12 yayin da wasu suka jikkata.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar halaka wani kasurgumin shugaban ƴan bindiga a jihar Zamfara. Sojojin sun kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.
Yan ta'adda
Samu kari