Kai Tsaye: Sakamakon Zaben Fitar da Gwanin APC tsakanin Tinubu da Osifor Ya Fara Fitowa

All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
2 Posts
Sort by
Ahmad Yusuf avatar Sani Hamza avatar
daga Ahmad Yusuf and Sani Hamza

Tinubu ya yi nasara a mazabar Stanley Osifo

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu gagarumar nasara a kan Stanley Osifo a zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam'iyyar All Progressives Congress (APC) da ya gudana a mazaɓa ta 9 ta Ute-Okpu, da ke Ƙaramar Hukumar Ika ta Arewa-Maso-Gabas a Jihar Delta.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa mambobin jam'iyyar APC sun fito kwansu da kwarkwata sun yi zabe a mazabar a yau Asabar.

Ahmad Yusuf avatar Sani Hamza avatar
daga Ahmad Yusuf and Sani Hamza

Zaben APC: Tinubu ya yi nasara a jihar Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a matsyain wanda ya lashe zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa.

Gwamnan, wanda shi ne shugaban kwamitin tattara sakamako ya sanar da hakan ne a wani faifan bidiyo da Imran Muhammad ya wallafa a X

Sakamakon da aka bayyana ya nuna cewa Tinubu ya samu ƙuri’u 321,579, yayin da abokin takararsa, Stanley Osifo, ya samu ƙuri’u 42 kacal.

Sakamakon zaben fitar da gwanin APC a Zamfara

Shugaba Bola Ahmed Tinubu - 321,579

Stanley Osifo - 42