Kai Tsaye: Sakamakon Zaben Fitar da Gwanin APC tsakanin Tinubu da Osifor Ya Fara Fitowa
Tinubu ya yi nasara a mazabar Stanley Osifo
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu gagarumar nasara a kan Stanley Osifo a zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam'iyyar All Progressives Congress (APC) da ya gudana a mazaɓa ta 9 ta Ute-Okpu, da ke Ƙaramar Hukumar Ika ta Arewa-Maso-Gabas a Jihar Delta.
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa mambobin jam'iyyar APC sun fito kwansu da kwarkwata sun yi zabe a mazabar a yau Asabar.
Zaben APC: Tinubu ya yi nasara a jihar Zamfara
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a matsyain wanda ya lashe zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa.
Gwamnan, wanda shi ne shugaban kwamitin tattara sakamako ya sanar da hakan ne a wani faifan bidiyo da Imran Muhammad ya wallafa a X
Sakamakon da aka bayyana ya nuna cewa Tinubu ya samu ƙuri’u 321,579, yayin da abokin takararsa, Stanley Osifo, ya samu ƙuri’u 42 kacal.
Sakamakon zaben fitar da gwanin APC a Zamfara
Shugaba Bola Ahmed Tinubu - 321,579
Stanley Osifo - 42