Domin Biyayya ga Umarnin Tinubu, Minista Ya Yi Murabus daga Mukaminsa a Najeriya
- Yayin da wa'adin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayar ke dab da cika, Yusuf Tuggar ya yi murabus daga kujerar ministan harkokin waje
- Tuggar ya dauki wannan mataki ne domin maida hankali ga burinsa na neman zama gwamnan jihar Bauchi a babban zaben 2027 da ke tafe
- Tun farko, Shugaba Tinubu ya umarci ministoci da duk wani jami'in gwamnati da ke shirin tsayawa takara ya yi murabus a ko kafin 31 ga Maris, 2026
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, ya yi murabus daga mukaminsa a yau Litinin, 30 ga watan Maris, 2026.
Rahotanni sun tabbatar da cewa Tuggar ya ajiye aiki ne domin ya nemi kujerar gwamnan Jihar Bauchi a babban zaɓe na 2027 mai zuwa.

Source: UGC
Yusuf Tuggar ya ajiye kujerar minista
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa ministan, wanda mamba ne a jam'iyyar APC mai mulki, ya mika takardar murabus daga mulaminsa ga shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Ya dauki wannan matakin ne sa'o'i 24 kafin cikar wa'adin da shugaban kasa ya bada ga duk wani mai rike da mukami da ke fa burin neman talara a babban zabe mai zuwa.
Umarnin da Shugaba Tinubu ya bayar
Idan baku manta ba, ya umurci duk wani jami’in gwamnatinsa da ke da niyyar tsayawa takara a zaɓe mai zuwa ya yi murabus xaga mukaminsa a ko kafin ranar 31 ga Maris, 2026.
Wannan umarni na Bola Tinubu ya fito ne daga ofishin Sakataran Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume.
Hakan ya yi daidai da sashi na 88(1) na Dokar Zaɓe ta 2026, da kuma jadawalin da Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) ta fitar na zaben fitar da yan takara da jam’iyyun siyasa za su gudanar gabanin 2027.

Source: Twitter
Dalilin murabus din Yusuf Tuggar
Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta tabbatar da murabus din Yusuf Tuggar ta hannun mai magana da yawunta, Kimiebi Ebienfa, a wata sanarwa da ta fitar yau Litinin.
Tuggar na daya daga cikin mimistocin da suke da niyyar neman kujerar gwamna a jihohinsu karkashin inuwar jam'iyyar APC mai mulki, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.
Tare da wannan ci gaba, ana sa ran samun karin murabus daga wasu ministoci da jami'an gwamnatin tarayya a kwanaki masu zuwa yayin da suke kokarin biyayya ga wa’adin da shugabann kasa ya ƙayyade.
Gawuna ya ajiye wa Tinubu mukaminsa
A wani rahoton, kun ji cewa Nasiru Yusuf.Gawuna, ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban kwamitin gudanarwa na Bankin Lamunin Gidaje na Ƙasa (FMBN).
Wannan na zuwa ne yayin da ake rade-radin Gawuna, wanda ya yi takarar gwamnan Kano a inuwar APC a zaben 2023, na shirin sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC tare da Kwankwaso.
Gawuna ya bayyana cewa murabus ɗin nasa ya fara aiki nan take, yana mai cewa matakin ya yi daidai da umarnin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Asali: Legit.ng

