Lamari Ya Lalace: 'Yan Bindiga Sun Kai Hari kan Peter Obi, Tsohon Shugaban APC
- Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi, da John Odigie-Oyegun tare da shugabannin ADC sun tsira daga harin ‘yan bindiga
- Dr Yunusa Tanko ya ce maharan sun bi su daga sakatariyar ADC zuwa gidan Odigie-Oyegun, inda suka harbe ƙofa tare da lalata motoci
- Lamarin ya faru yayin shigar Olumide Akpata ADC, yana ƙara zafi a siyasar Edo bayan takaddama kan sakamakon zaɓen AMAC
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Edo - Yan bindiga sun kai hari kan tsohon dan takarar shugaban kasa a 2023, Peter Obi da wasu jigaj-jigan ADC a jihar Edo.
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi, da tsohon shugaban APC na ƙasa, John Odigie-Oyegun, tare da wasu shugabannin ADC suka gamu da harin.
Mai magana da yawun kamfen Obi a baya kuma mai kula da Obidient Movement na duniya, Dr Yunusa Tanko, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da Punch ta samu.

Kara karanta wannan
Tashin hankali: 'Yan bindiga sun farmaki Peter Obi, an yi yunkurin kashe shi a Benin
Sanarwar ta ce:
“Peter Obi da shugabannin ADC na cikin kewaye da hari a Benin, Edo, a lokacin shigar Olumide Akpata ADC, wasu dauke da makamai sun bi mu.”
Ya ce sun bi tawagar daga sakatariyar ADC zuwa gidan John Odigie-Oyegun, inda suka harbe ƙofa tare da lalata motoci da dama a harin.
Tanko ya bayyana lamarin a matsayin yunƙurin kashe su da bai yi nasara ba, yana mai cewa dimokuraɗiyya na cikin haɗari a ƙasar.
Hotuna da bidiyo da aka aiko sun nuna gilasan motocin SUV sun farfashe, yayin da ƙofar gidan Odigie-Oyegun ta cika da ramukan harsashi.
An ce harin ya faru ne yayin harkokin siyasa na shigar Olumide Akpata ADC, abin da ya ƙara tada hankali a siyasar Edo.
Rahoton ya ce lamarin ya zo ne kwana guda bayan ɗan takarar ADC na shugabancin AMAC, Dr Moses Paul, ya ƙi amincewa da sakamakon zaɓe.
Hukumar INEC ta bayyana Christopher Maikalangu na APC a matsayin wanda ya yi nasara da kuri’u 40,295 cikin 62,861 ingantattun kuri’u.
Paul ya zo na biyu da kuri’u 12,109, yayin da ɗan takarar PDP ya samu kuri’u 3,398 a zaɓen.
Sai dai Paul ya zargi INEC da tabka kura-kurai, yana ambaton danniya ga masu zaɓe, magudin sakamako, tsoratarwa da sayen kuri’u a unguwanni.
Karin bayani na tafe....
Asali: Legit.ng
